• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Karbe Ikon Kauyuka 400 A Zamfara -Masani

by Sadiq
2 years ago
Zamfara

Wani masani kan harkokin tsaro a jihar Zamfara, Buhari Abubakar, ya bayyana damuwarsa kan yadda kashe-kashe da sace-sacen jama’a ke sake tabarbarewa, inda ya zargi cewa sama da kauyuka 400 ne ke karkashin ikon ‘yan ta’adda.

A wata hira ta musamman, Abubakar ya yi mamakin dalilin da ya sa shugaban kasa Bola Tinubu ke tura rundunar soji zuwa Jamhuriyar Nijar, maimakon mayar da hankali kan barazanar tsaro da ‘yan Nijeriya ke fuskanta.

  • Yanzu-Yanzu: Masallacin Fadar Sarkin Zazzau Ya Rufta Da Mutane Yayin Sallar La’asar
  • Kofin Duniya: Abin Da Ya Biyo Bayan Cire Nijeriya Daga Gasar

A cewarsa, ya kamata gwamnatin tarayya da na jihohi su yi taka tsan-tsan wajen ganin an shawo kan matsalar rashin tsaro a jihar Zamfara, domin ‘yan fashin sun kara karfi fiye da da.

Ya kara da cewa, “Duk wanda ya yi riya cewa komai ya daidaita a jihar Zamfara, yana yaudarar kansa ne, domin mazauna garin ba suma barci cikin salama sama da shekaru goma,” in ji shi.

Ya ce, bisa kididdigar da aka yi, akalla kauyuka 400 ne ke hannun ‘yan bindiga a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

“’Yan ta’addan sun kafa gwamnatinsu a wadannan yankunan, kuma su ne suke yanke shawarar abin da zai faru da abin da ya kamata a yi a cikin al’ummomin da suke rike da su.

“Mutanen yankin sun san wadannan ‘yan fashi da maboyarsu amma ba za su iya magana ko fallasa su ba saboda fargaba, ‘yan bindigar sun sha gargadin kada su yi magana da wani dan jarida, idan ba haka ba za a kai musu hari.

A cewarsa, tsaron rayuka da dukiyoyin ’yan Nijeriya na kan wuyan gwamnatin tarayya ba gwamnatin jiha ba kamar yadda mutane da yawa suka fahimta.

“Gwamnatin Jihohi na ba jami’an tsaro kayan aiki ne kawai don ba su damar gudanar da ayyukansu na tabbatar da rayuka da dukiyoyin ‘yan kasa cikin sauki.

“Ko shakka babu jihar Zamfara ta zama mamayar ‘yan fashi a fadin kasar nan, yawan kashe-kashe da garkuwa da mutane da fyade ya zama ruwan dare.

“Akwai bayanai sun nuna a fili cewa akwai dubban zawarawa da marayu da ke yawo a kan tituna ba tare da wata manufa ba saboda ‘yan fashi da suka kashe mazajensu da iyayensu, wanda hakan ya sa suka zama almajirai da karuwai.

“Muna rayuwa cikin wani mummunan hali kamar ba mu da gwamnati ko jami’an tsaro a jihar kuma gwamnatoci da shugabannin tsaro suna kallo kamar babu abin da ke faruwa.

Abubakar ya ci gaba da bayanin cewa gwamnatin tarayya da na jihohi ba za su iya dakatar da wadannan kashe-kashe da sace-sacen mutane da fyade ba, idan ba a dauki tsauraran matakai ba, yana mai nuni da cewa akwai masu fada a ji a cikin wadannan munanan ayyuka, yana mai cewa ‘yan fashin ba su kadai suke yi ba.

Ya shawarci gwamnatocin tarayya da na jihohi da su farka daga barcin da suke yi, su magance tsatsauran ra’ayi da duk wanda ke da hannu a cikin ta’addanci.

“Ayyukan ‘yan fashi sun jawo asarar dubban rayuka da karancin abinci yayin da manoma ba sa gudanar da ayyukansu na noma a jihar.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI
Labarai

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Labarai

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Next Post
Ofishin Jakadancin Sin A Ghana Ya Bude Cibiyar Bayar Da Visa

Ofishin Jakadancin Sin A Ghana Ya Bude Cibiyar Bayar Da Visa

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.