• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Karbe Ikon Kauyuka 400 A Zamfara -Masani

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
‘Yan Bindiga Sun Karbe Ikon Kauyuka 400 A Zamfara -Masani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani masani kan harkokin tsaro a jihar Zamfara, Buhari Abubakar, ya bayyana damuwarsa kan yadda kashe-kashe da sace-sacen jama’a ke sake tabarbarewa, inda ya zargi cewa sama da kauyuka 400 ne ke karkashin ikon ‘yan ta’adda.

A wata hira ta musamman, Abubakar ya yi mamakin dalilin da ya sa shugaban kasa Bola Tinubu ke tura rundunar soji zuwa Jamhuriyar Nijar, maimakon mayar da hankali kan barazanar tsaro da ‘yan Nijeriya ke fuskanta.

  • Yanzu-Yanzu: Masallacin Fadar Sarkin Zazzau Ya Rufta Da Mutane Yayin Sallar La’asar
  • Kofin Duniya: Abin Da Ya Biyo Bayan Cire Nijeriya Daga Gasar

A cewarsa, ya kamata gwamnatin tarayya da na jihohi su yi taka tsan-tsan wajen ganin an shawo kan matsalar rashin tsaro a jihar Zamfara, domin ‘yan fashin sun kara karfi fiye da da.

Ya kara da cewa, “Duk wanda ya yi riya cewa komai ya daidaita a jihar Zamfara, yana yaudarar kansa ne, domin mazauna garin ba suma barci cikin salama sama da shekaru goma,” in ji shi.

Ya ce, bisa kididdigar da aka yi, akalla kauyuka 400 ne ke hannun ‘yan bindiga a jihar.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

“’Yan ta’addan sun kafa gwamnatinsu a wadannan yankunan, kuma su ne suke yanke shawarar abin da zai faru da abin da ya kamata a yi a cikin al’ummomin da suke rike da su.

“Mutanen yankin sun san wadannan ‘yan fashi da maboyarsu amma ba za su iya magana ko fallasa su ba saboda fargaba, ‘yan bindigar sun sha gargadin kada su yi magana da wani dan jarida, idan ba haka ba za a kai musu hari.

A cewarsa, tsaron rayuka da dukiyoyin ’yan Nijeriya na kan wuyan gwamnatin tarayya ba gwamnatin jiha ba kamar yadda mutane da yawa suka fahimta.

“Gwamnatin Jihohi na ba jami’an tsaro kayan aiki ne kawai don ba su damar gudanar da ayyukansu na tabbatar da rayuka da dukiyoyin ‘yan kasa cikin sauki.

“Ko shakka babu jihar Zamfara ta zama mamayar ‘yan fashi a fadin kasar nan, yawan kashe-kashe da garkuwa da mutane da fyade ya zama ruwan dare.

“Akwai bayanai sun nuna a fili cewa akwai dubban zawarawa da marayu da ke yawo a kan tituna ba tare da wata manufa ba saboda ‘yan fashi da suka kashe mazajensu da iyayensu, wanda hakan ya sa suka zama almajirai da karuwai.

“Muna rayuwa cikin wani mummunan hali kamar ba mu da gwamnati ko jami’an tsaro a jihar kuma gwamnatoci da shugabannin tsaro suna kallo kamar babu abin da ke faruwa.

Abubakar ya ci gaba da bayanin cewa gwamnatin tarayya da na jihohi ba za su iya dakatar da wadannan kashe-kashe da sace-sacen mutane da fyade ba, idan ba a dauki tsauraran matakai ba, yana mai nuni da cewa akwai masu fada a ji a cikin wadannan munanan ayyuka, yana mai cewa ‘yan fashin ba su kadai suke yi ba.

Ya shawarci gwamnatocin tarayya da na jihohi da su farka daga barcin da suke yi, su magance tsatsauran ra’ayi da duk wanda ke da hannu a cikin ta’addanci.

“Ayyukan ‘yan fashi sun jawo asarar dubban rayuka da karancin abinci yayin da manoma ba sa gudanar da ayyukansu na noma a jihar.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MasaniYan bindigaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Kara Ware Yuan Biliyan 1.46 Don Taimakawa Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

Next Post

Ofishin Jakadancin Sin A Ghana Ya Bude Cibiyar Bayar Da Visa

Related

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

4 minutes ago
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

14 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

15 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

16 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

16 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

18 hours ago
Next Post
Ofishin Jakadancin Sin A Ghana Ya Bude Cibiyar Bayar Da Visa

Ofishin Jakadancin Sin A Ghana Ya Bude Cibiyar Bayar Da Visa

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.