ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Karbe Ikon Kauyuka 400 A Zamfara -Masani

by Sadiq
3 years ago
Zamfara

Wani masani kan harkokin tsaro a jihar Zamfara, Buhari Abubakar, ya bayyana damuwarsa kan yadda kashe-kashe da sace-sacen jama’a ke sake tabarbarewa, inda ya zargi cewa sama da kauyuka 400 ne ke karkashin ikon ‘yan ta’adda.

A wata hira ta musamman, Abubakar ya yi mamakin dalilin da ya sa shugaban kasa Bola Tinubu ke tura rundunar soji zuwa Jamhuriyar Nijar, maimakon mayar da hankali kan barazanar tsaro da ‘yan Nijeriya ke fuskanta.

  • Yanzu-Yanzu: Masallacin Fadar Sarkin Zazzau Ya Rufta Da Mutane Yayin Sallar La’asar
  • Kofin Duniya: Abin Da Ya Biyo Bayan Cire Nijeriya Daga Gasar

A cewarsa, ya kamata gwamnatin tarayya da na jihohi su yi taka tsan-tsan wajen ganin an shawo kan matsalar rashin tsaro a jihar Zamfara, domin ‘yan fashin sun kara karfi fiye da da.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, “Duk wanda ya yi riya cewa komai ya daidaita a jihar Zamfara, yana yaudarar kansa ne, domin mazauna garin ba suma barci cikin salama sama da shekaru goma,” in ji shi.

Ya ce, bisa kididdigar da aka yi, akalla kauyuka 400 ne ke hannun ‘yan bindiga a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

“’Yan ta’addan sun kafa gwamnatinsu a wadannan yankunan, kuma su ne suke yanke shawarar abin da zai faru da abin da ya kamata a yi a cikin al’ummomin da suke rike da su.

“Mutanen yankin sun san wadannan ‘yan fashi da maboyarsu amma ba za su iya magana ko fallasa su ba saboda fargaba, ‘yan bindigar sun sha gargadin kada su yi magana da wani dan jarida, idan ba haka ba za a kai musu hari.

A cewarsa, tsaron rayuka da dukiyoyin ’yan Nijeriya na kan wuyan gwamnatin tarayya ba gwamnatin jiha ba kamar yadda mutane da yawa suka fahimta.

“Gwamnatin Jihohi na ba jami’an tsaro kayan aiki ne kawai don ba su damar gudanar da ayyukansu na tabbatar da rayuka da dukiyoyin ‘yan kasa cikin sauki.

“Ko shakka babu jihar Zamfara ta zama mamayar ‘yan fashi a fadin kasar nan, yawan kashe-kashe da garkuwa da mutane da fyade ya zama ruwan dare.

“Akwai bayanai sun nuna a fili cewa akwai dubban zawarawa da marayu da ke yawo a kan tituna ba tare da wata manufa ba saboda ‘yan fashi da suka kashe mazajensu da iyayensu, wanda hakan ya sa suka zama almajirai da karuwai.

“Muna rayuwa cikin wani mummunan hali kamar ba mu da gwamnati ko jami’an tsaro a jihar kuma gwamnatoci da shugabannin tsaro suna kallo kamar babu abin da ke faruwa.

Abubakar ya ci gaba da bayanin cewa gwamnatin tarayya da na jihohi ba za su iya dakatar da wadannan kashe-kashe da sace-sacen mutane da fyade ba, idan ba a dauki tsauraran matakai ba, yana mai nuni da cewa akwai masu fada a ji a cikin wadannan munanan ayyuka, yana mai cewa ‘yan fashin ba su kadai suke yi ba.

Ya shawarci gwamnatocin tarayya da na jihohi da su farka daga barcin da suke yi, su magance tsatsauran ra’ayi da duk wanda ke da hannu a cikin ta’addanci.

“Ayyukan ‘yan fashi sun jawo asarar dubban rayuka da karancin abinci yayin da manoma ba sa gudanar da ayyukansu na noma a jihar.”

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Ofishin Jakadancin Sin A Ghana Ya Bude Cibiyar Bayar Da Visa

Ofishin Jakadancin Sin A Ghana Ya Bude Cibiyar Bayar Da Visa

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.