ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Karbe Ikon Kauyuka 400 A Zamfara -Masani

by Sadiq
3 years ago
Zamfara

Wani masani kan harkokin tsaro a jihar Zamfara, Buhari Abubakar, ya bayyana damuwarsa kan yadda kashe-kashe da sace-sacen jama’a ke sake tabarbarewa, inda ya zargi cewa sama da kauyuka 400 ne ke karkashin ikon ‘yan ta’adda.

A wata hira ta musamman, Abubakar ya yi mamakin dalilin da ya sa shugaban kasa Bola Tinubu ke tura rundunar soji zuwa Jamhuriyar Nijar, maimakon mayar da hankali kan barazanar tsaro da ‘yan Nijeriya ke fuskanta.

  • Yanzu-Yanzu: Masallacin Fadar Sarkin Zazzau Ya Rufta Da Mutane Yayin Sallar La’asar
  • Kofin Duniya: Abin Da Ya Biyo Bayan Cire Nijeriya Daga Gasar

A cewarsa, ya kamata gwamnatin tarayya da na jihohi su yi taka tsan-tsan wajen ganin an shawo kan matsalar rashin tsaro a jihar Zamfara, domin ‘yan fashin sun kara karfi fiye da da.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, “Duk wanda ya yi riya cewa komai ya daidaita a jihar Zamfara, yana yaudarar kansa ne, domin mazauna garin ba suma barci cikin salama sama da shekaru goma,” in ji shi.

Ya ce, bisa kididdigar da aka yi, akalla kauyuka 400 ne ke hannun ‘yan bindiga a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

“’Yan ta’addan sun kafa gwamnatinsu a wadannan yankunan, kuma su ne suke yanke shawarar abin da zai faru da abin da ya kamata a yi a cikin al’ummomin da suke rike da su.

“Mutanen yankin sun san wadannan ‘yan fashi da maboyarsu amma ba za su iya magana ko fallasa su ba saboda fargaba, ‘yan bindigar sun sha gargadin kada su yi magana da wani dan jarida, idan ba haka ba za a kai musu hari.

A cewarsa, tsaron rayuka da dukiyoyin ’yan Nijeriya na kan wuyan gwamnatin tarayya ba gwamnatin jiha ba kamar yadda mutane da yawa suka fahimta.

“Gwamnatin Jihohi na ba jami’an tsaro kayan aiki ne kawai don ba su damar gudanar da ayyukansu na tabbatar da rayuka da dukiyoyin ‘yan kasa cikin sauki.

“Ko shakka babu jihar Zamfara ta zama mamayar ‘yan fashi a fadin kasar nan, yawan kashe-kashe da garkuwa da mutane da fyade ya zama ruwan dare.

“Akwai bayanai sun nuna a fili cewa akwai dubban zawarawa da marayu da ke yawo a kan tituna ba tare da wata manufa ba saboda ‘yan fashi da suka kashe mazajensu da iyayensu, wanda hakan ya sa suka zama almajirai da karuwai.

“Muna rayuwa cikin wani mummunan hali kamar ba mu da gwamnati ko jami’an tsaro a jihar kuma gwamnatoci da shugabannin tsaro suna kallo kamar babu abin da ke faruwa.

Abubakar ya ci gaba da bayanin cewa gwamnatin tarayya da na jihohi ba za su iya dakatar da wadannan kashe-kashe da sace-sacen mutane da fyade ba, idan ba a dauki tsauraran matakai ba, yana mai nuni da cewa akwai masu fada a ji a cikin wadannan munanan ayyuka, yana mai cewa ‘yan fashin ba su kadai suke yi ba.

Ya shawarci gwamnatocin tarayya da na jihohi da su farka daga barcin da suke yi, su magance tsatsauran ra’ayi da duk wanda ke da hannu a cikin ta’addanci.

“Ayyukan ‘yan fashi sun jawo asarar dubban rayuka da karancin abinci yayin da manoma ba sa gudanar da ayyukansu na noma a jihar.”

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Ofishin Jakadancin Sin A Ghana Ya Bude Cibiyar Bayar Da Visa

Ofishin Jakadancin Sin A Ghana Ya Bude Cibiyar Bayar Da Visa

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.