ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kofin Duniya: Abin Da Ya Biyo Bayan Cire Nijeriya Daga Gasar

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Tawagar ‘yan wasa ta kwallon kafar mata ta dawo gida bayan rashin nasara da suka yi a hannun kasar Ingila a wasan faradda da kasashen suka fafata a gasar cin kofin duniya da a yanzu haka take gudana a kasashen Australia da New Zealand.

Nijeriya ta fito a cikin rukunin da ya hada kasashen Kanada da Jamhuriyar Irland da kuma mai masaukin baki Australia, kuma duk da haka ta samu damar fitowa daga cikin rukuni a mataki na biyu bayan ta samu nasara a wasa daya, sannan ta yi canjaras a wasanni biyu wanda hakan ya sa ta hada maki biyar.

  • Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka Na Kara Haifar Da Da Mai Ido
  • Ba Zan yi Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ba, Cewar Dikko Radda

Sai dai ta yi rashin nasara a wasan da tawagar ta kece raini da tawagar Ingila, wadda ta doke Super Falcons din ta Nijeriya a bugun daga kai sai mai tsaron raga bayan an tashi daga wasan babu kasar da ta zura kwallo a ragar ‘yar uwarta.

Wannan shi ne karo na tara da tawagar Nijeriya take zuwa gasar cin kofin duniya tun daga shekara ta 1991 da ta fara zuwa, inda tawagar ta buga wasanni 29 tun daga shekarar da ta fara zuwa gasar ta samu nasara a wasanni biyar ta yi canjaras sau biyar, sannan ta yi rashin nasara a wasanni 19, sai aka zura mata kwallaye 65 ita kuma ta zura guda 23.

Sai dai duk da haka Nijeriya ce kasa ta farko daga Nahiyar Afirka da ta je wasan kusa da na karshe a gasar cin kofin duniya da kuma gasar guje-guje da tsalle-tsalle ta Olympic.

Har ila yau, Nijeriya ce tafi kowacce kasa a Nahiyar Afirka yawan lashe gasar cin kofin Nahiyar Afirka ta mata, inda ta lashe gasar sau 11 a tarihi.

Kin Biyan Albashi Da Alawus Din ‘Yan Wasa

Har yanzu ‘yan wasan ba su karbi albashin da suke bin hukumar kwallon kafa ta kasa ba da kuma ragowar hakkokinsu wanda tuni wasu daga cikin tsofaffin ‘yan wasan Nijeriya maza suka bayyana rashin jin dadinsu da wannan al’ada ta Nijeriya ta kin biyan ‘yan wasa hakkokinsu.

Dan wasan Napoli, Bictor Osimhen da tsohon dan wasan Eberton, Bictor Anichebe duka sun nuna rashin jin dadinsu na kin biyan ‘yan wasa mata kudinsu, sannan shi ma dan wasa Odion Ighalo ya bayyana takaicinsa na kin biyansu kudinsu.

Sai dai hukumar kwallon kafa ta kasa (NFF) ta bayyana cewa za ta biya kudin nan ba da jimawa ba kuma sun yi alkawari da ‘yan wasan cewa sai an gama gasar za su karbi kudadisu, sannan kuma ‘yan wasan sun amince da hakan.

Nijeriya
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Next Post
Yanzu-Yanzu: Masallacin Fadar Sarkin Zazzau Ya Rufta Da Mutane Yayin Sallar La’asar

Yanzu-Yanzu: Masallacin Fadar Sarkin Zazzau Ya Rufta Da Mutane Yayin Sallar La’asar

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.