ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kofin Duniya: Abin Da Ya Biyo Bayan Cire Nijeriya Daga Gasar

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

Tawagar ‘yan wasa ta kwallon kafar mata ta dawo gida bayan rashin nasara da suka yi a hannun kasar Ingila a wasan faradda da kasashen suka fafata a gasar cin kofin duniya da a yanzu haka take gudana a kasashen Australia da New Zealand.

Nijeriya ta fito a cikin rukunin da ya hada kasashen Kanada da Jamhuriyar Irland da kuma mai masaukin baki Australia, kuma duk da haka ta samu damar fitowa daga cikin rukuni a mataki na biyu bayan ta samu nasara a wasa daya, sannan ta yi canjaras a wasanni biyu wanda hakan ya sa ta hada maki biyar.

  • Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka Na Kara Haifar Da Da Mai Ido
  • Ba Zan yi Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ba, Cewar Dikko Radda

Sai dai ta yi rashin nasara a wasan da tawagar ta kece raini da tawagar Ingila, wadda ta doke Super Falcons din ta Nijeriya a bugun daga kai sai mai tsaron raga bayan an tashi daga wasan babu kasar da ta zura kwallo a ragar ‘yar uwarta.

Wannan shi ne karo na tara da tawagar Nijeriya take zuwa gasar cin kofin duniya tun daga shekara ta 1991 da ta fara zuwa, inda tawagar ta buga wasanni 29 tun daga shekarar da ta fara zuwa gasar ta samu nasara a wasanni biyar ta yi canjaras sau biyar, sannan ta yi rashin nasara a wasanni 19, sai aka zura mata kwallaye 65 ita kuma ta zura guda 23.

Sai dai duk da haka Nijeriya ce kasa ta farko daga Nahiyar Afirka da ta je wasan kusa da na karshe a gasar cin kofin duniya da kuma gasar guje-guje da tsalle-tsalle ta Olympic.

Har ila yau, Nijeriya ce tafi kowacce kasa a Nahiyar Afirka yawan lashe gasar cin kofin Nahiyar Afirka ta mata, inda ta lashe gasar sau 11 a tarihi.

Kin Biyan Albashi Da Alawus Din ‘Yan Wasa

Har yanzu ‘yan wasan ba su karbi albashin da suke bin hukumar kwallon kafa ta kasa ba da kuma ragowar hakkokinsu wanda tuni wasu daga cikin tsofaffin ‘yan wasan Nijeriya maza suka bayyana rashin jin dadinsu da wannan al’ada ta Nijeriya ta kin biyan ‘yan wasa hakkokinsu.

Dan wasan Napoli, Bictor Osimhen da tsohon dan wasan Eberton, Bictor Anichebe duka sun nuna rashin jin dadinsu na kin biyan ‘yan wasa mata kudinsu, sannan shi ma dan wasa Odion Ighalo ya bayyana takaicinsa na kin biyansu kudinsu.

Sai dai hukumar kwallon kafa ta kasa (NFF) ta bayyana cewa za ta biya kudin nan ba da jimawa ba kuma sun yi alkawari da ‘yan wasan cewa sai an gama gasar za su karbi kudadisu, sannan kuma ‘yan wasan sun amince da hakan.

Nijeriya
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji
  • Abba Ibrahim Wada
    Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City
  • Abba Ibrahim Wada
    LeBron James Zai Bar Los Angeles Lakers 
  • Abba Ibrahim Wada
    An Raba Jadawalin Gasar Premier Ta Ingila Ta Kakar Wasan 2026/2027
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji
Wasanni

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA
Wasanni

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa
Wasanni

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Next Post
Yanzu-Yanzu: Masallacin Fadar Sarkin Zazzau Ya Rufta Da Mutane Yayin Sallar La’asar

Yanzu-Yanzu: Masallacin Fadar Sarkin Zazzau Ya Rufta Da Mutane Yayin Sallar La’asar

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

July 9, 2026
Auto Draft

TCN Ta Kammala Gyaran Layin Wutar Lantarkin Zaria–Funtua 132kV

July 9, 2026
Auto Draft

DSS Ta Kama ‘Yar Jarida Zainab Sodiq Kan Zargin Mallakar Drone Ba Tare da Cikakkun Takardu ba

July 9, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

July 9, 2026
Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

July 9, 2026
’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A  Jihar Benuwai

’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A Jihar Benuwai

July 9, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

Sojoji Sun Hallaka Shugaban ’Yan Bindiga, Sun Daƙile Hare-hare A Zamfara

July 9, 2026
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026
Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.