ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kofin Duniya: Abin Da Ya Biyo Bayan Cire Nijeriya Daga Gasar

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Tawagar ‘yan wasa ta kwallon kafar mata ta dawo gida bayan rashin nasara da suka yi a hannun kasar Ingila a wasan faradda da kasashen suka fafata a gasar cin kofin duniya da a yanzu haka take gudana a kasashen Australia da New Zealand.

Nijeriya ta fito a cikin rukunin da ya hada kasashen Kanada da Jamhuriyar Irland da kuma mai masaukin baki Australia, kuma duk da haka ta samu damar fitowa daga cikin rukuni a mataki na biyu bayan ta samu nasara a wasa daya, sannan ta yi canjaras a wasanni biyu wanda hakan ya sa ta hada maki biyar.

  • Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka Na Kara Haifar Da Da Mai Ido
  • Ba Zan yi Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ba, Cewar Dikko Radda

Sai dai ta yi rashin nasara a wasan da tawagar ta kece raini da tawagar Ingila, wadda ta doke Super Falcons din ta Nijeriya a bugun daga kai sai mai tsaron raga bayan an tashi daga wasan babu kasar da ta zura kwallo a ragar ‘yar uwarta.

Wannan shi ne karo na tara da tawagar Nijeriya take zuwa gasar cin kofin duniya tun daga shekara ta 1991 da ta fara zuwa, inda tawagar ta buga wasanni 29 tun daga shekarar da ta fara zuwa gasar ta samu nasara a wasanni biyar ta yi canjaras sau biyar, sannan ta yi rashin nasara a wasanni 19, sai aka zura mata kwallaye 65 ita kuma ta zura guda 23.

Sai dai duk da haka Nijeriya ce kasa ta farko daga Nahiyar Afirka da ta je wasan kusa da na karshe a gasar cin kofin duniya da kuma gasar guje-guje da tsalle-tsalle ta Olympic.

Har ila yau, Nijeriya ce tafi kowacce kasa a Nahiyar Afirka yawan lashe gasar cin kofin Nahiyar Afirka ta mata, inda ta lashe gasar sau 11 a tarihi.

Kin Biyan Albashi Da Alawus Din ‘Yan Wasa

Har yanzu ‘yan wasan ba su karbi albashin da suke bin hukumar kwallon kafa ta kasa ba da kuma ragowar hakkokinsu wanda tuni wasu daga cikin tsofaffin ‘yan wasan Nijeriya maza suka bayyana rashin jin dadinsu da wannan al’ada ta Nijeriya ta kin biyan ‘yan wasa hakkokinsu.

Dan wasan Napoli, Bictor Osimhen da tsohon dan wasan Eberton, Bictor Anichebe duka sun nuna rashin jin dadinsu na kin biyan ‘yan wasa mata kudinsu, sannan shi ma dan wasa Odion Ighalo ya bayyana takaicinsa na kin biyansu kudinsu.

Sai dai hukumar kwallon kafa ta kasa (NFF) ta bayyana cewa za ta biya kudin nan ba da jimawa ba kuma sun yi alkawari da ‘yan wasan cewa sai an gama gasar za su karbi kudadisu, sannan kuma ‘yan wasan sun amince da hakan.

Nijeriya
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?
  • Abba Ibrahim Wada
    Jiya Aka Fara Gasar Cin Kofin Duniya
  • Abba Ibrahim Wada
    Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya
  • Abba Ibrahim Wada
    Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé
Wasanni

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?
Wasanni

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Real Madrid Ta Kammala Ɗaukar Bernardo Silva Daga Man City
Wasanni

Real Madrid Ta Kammala Ɗaukar Bernardo Silva Daga Man City

June 12, 2026
Next Post
Yanzu-Yanzu: Masallacin Fadar Sarkin Zazzau Ya Rufta Da Mutane Yayin Sallar La’asar

Yanzu-Yanzu: Masallacin Fadar Sarkin Zazzau Ya Rufta Da Mutane Yayin Sallar La’asar

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.