ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kofin Duniya: Abin Da Ya Biyo Bayan Cire Nijeriya Daga Gasar

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

Tawagar ‘yan wasa ta kwallon kafar mata ta dawo gida bayan rashin nasara da suka yi a hannun kasar Ingila a wasan faradda da kasashen suka fafata a gasar cin kofin duniya da a yanzu haka take gudana a kasashen Australia da New Zealand.

Nijeriya ta fito a cikin rukunin da ya hada kasashen Kanada da Jamhuriyar Irland da kuma mai masaukin baki Australia, kuma duk da haka ta samu damar fitowa daga cikin rukuni a mataki na biyu bayan ta samu nasara a wasa daya, sannan ta yi canjaras a wasanni biyu wanda hakan ya sa ta hada maki biyar.

  • Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka Na Kara Haifar Da Da Mai Ido
  • Ba Zan yi Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ba, Cewar Dikko Radda

Sai dai ta yi rashin nasara a wasan da tawagar ta kece raini da tawagar Ingila, wadda ta doke Super Falcons din ta Nijeriya a bugun daga kai sai mai tsaron raga bayan an tashi daga wasan babu kasar da ta zura kwallo a ragar ‘yar uwarta.

Wannan shi ne karo na tara da tawagar Nijeriya take zuwa gasar cin kofin duniya tun daga shekara ta 1991 da ta fara zuwa, inda tawagar ta buga wasanni 29 tun daga shekarar da ta fara zuwa gasar ta samu nasara a wasanni biyar ta yi canjaras sau biyar, sannan ta yi rashin nasara a wasanni 19, sai aka zura mata kwallaye 65 ita kuma ta zura guda 23.

Sai dai duk da haka Nijeriya ce kasa ta farko daga Nahiyar Afirka da ta je wasan kusa da na karshe a gasar cin kofin duniya da kuma gasar guje-guje da tsalle-tsalle ta Olympic.

Har ila yau, Nijeriya ce tafi kowacce kasa a Nahiyar Afirka yawan lashe gasar cin kofin Nahiyar Afirka ta mata, inda ta lashe gasar sau 11 a tarihi.

Kin Biyan Albashi Da Alawus Din ‘Yan Wasa

Har yanzu ‘yan wasan ba su karbi albashin da suke bin hukumar kwallon kafa ta kasa ba da kuma ragowar hakkokinsu wanda tuni wasu daga cikin tsofaffin ‘yan wasan Nijeriya maza suka bayyana rashin jin dadinsu da wannan al’ada ta Nijeriya ta kin biyan ‘yan wasa hakkokinsu.

Dan wasan Napoli, Bictor Osimhen da tsohon dan wasan Eberton, Bictor Anichebe duka sun nuna rashin jin dadinsu na kin biyan ‘yan wasa mata kudinsu, sannan shi ma dan wasa Odion Ighalo ya bayyana takaicinsa na kin biyansu kudinsu.

Sai dai hukumar kwallon kafa ta kasa (NFF) ta bayyana cewa za ta biya kudin nan ba da jimawa ba kuma sun yi alkawari da ‘yan wasan cewa sai an gama gasar za su karbi kudadisu, sannan kuma ‘yan wasan sun amince da hakan.

Nijeriya
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Yaushe Za A Fara Kofin Zakarun Turai
  • Abba Ibrahim Wada
    Messi Ya Yi Ritaya A Argentina: Da Me Za Mu Iya Tuna Gwarzon Duniyar?
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye ‘Yan wasan Nijeriya Da Za Su Buga Gasar Firimiyar Ingila Ta Bana?
  • Abba Ibrahim Wada
    Chelsea A Ƙarƙashin Xavi Alonso
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
Wasanni

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

September 8, 2026
Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
Wasanni

Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain

September 7, 2026
Next Post
Yanzu-Yanzu: Masallacin Fadar Sarkin Zazzau Ya Rufta Da Mutane Yayin Sallar La’asar

Yanzu-Yanzu: Masallacin Fadar Sarkin Zazzau Ya Rufta Da Mutane Yayin Sallar La’asar

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.