Wasu ‘yan bindiga sun kashe ‘yan sa-kai guda huɗu da kuma wasu manoma da ba a tantance adadinsu ba a ƙauyen Marmara da ke ƙaramar hukumar Malumfashi a Jihar Katsina.
Harin ya faru ne da yammacin ranar Litinin a ƙauyen, inda mutane da dama suka jikkata.
- Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran
- Dalilin Mara Wa Tinubu Baya Ba Tare da Ambaton Shettima Ba – Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas
Wani masani a harkar tsaro mai suna Bakatsine ne ya bayyana hakan a shafinsa na X a ranar Talata.
Ya rubuta cewa: “Gargaɗi, da yammacin jiya, ‘yan bindiga sun kai wa manoma hari a ƙauyen Marmara, a ƙaramar hukumar Malumfashi a Jihar Katsina.
“Sun kashe jami’an tsaron CWC guda huɗu da ke taimakawa manoman. Haka kuma an kashe wasu manoman da dama, wasu kuma sun jikkata.”
Jaridar LEADERSHIP ta ruwaito cewa gwamnatin Jihar Katsina na ƙoƙarin sasantawa da wasu ƙungiyoyin ‘yan bindiga a wasu yankunan jihar.
Wasu daga cikin ‘yan bindigar da ke Jibia, Batsari da DanMusa sun amince da zaman lafiya tare da miƙa makamansu.
Sai dai wannan hari na baya-bayan nan ya sa al’umma sun fara shakkar ko zaman lafiyar zai ɗore.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp