Wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wane ne ba a ranar Laraba sun kashe wani mataimakin Sufeton ‘yan sanda a garin Oyigbo da ke karamar hukumar Oyigbo a Jihar Ribas.
An rawaito cewa jami’an ‘yan sandan da har yanzu ba a tantance ba ‘yan bindigar sun yi masa kwanton bauna ne a yayin da ya ke komawa gida bayan ya tashi daga aiki.
- ‘Yan Bindiga Sun Kashe ‘Yan Sanda, Sun Sace ‘Yan China 4 A Wajen Hakar Na’adinai A Neja
- 2023: Bayan Buhari, Dole Dan Kudu Ya Zama Shugaban Kasa – Fayose
Daga baya ya rasu a wani asibiti da ba a bayyana sunansa ba a yankin.
Sai dai babu wata kungiya da ta dauki alhakin kisan babban jami’in ‘yan sandan.
Da aka tuntubi kakakin ‘yan sandan jihar, Grace Iringe-Koko, ta tabbatar da faruwar lamarin.
Iringe-Koko ta bayyana cewa Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Eboka Friday, ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan kisan dan sandan.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp