• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutam 8 A Kofar Shiga Barikin Sojoji Da Ke Taraba

by Muhammad
2 years ago
'Yan Bindiga

Akalla mutane takwas ne aka kashe a yammacin ranar Litinin a bataliya ta 83 da ke Barikin Sojojin Ada a Takum hedikwatar karamar hukumar Takum a jihar Taraba.

Wadanda aka kashe din dai mutanen kauyen Jenuwa Nyafiye ne, wata kabilar Kutep da ke daura da kofar Sojojin. An ce suna dawowa ne daga daya daga cikin wuraren ibadar da ke yankin.

  • An Kashe Mutum 3 A Rikicin Kabilanci A Taraba
  • Rikicin Addini: An Sanya Dokar Hana Fita A Jihar Taraba

Daya daga cikin sarakunan yankin, Cif Godson Danlami Wasa, wanda ya zanta da wakilinmu ya bayyana cewa ‘yan bindiga ne suka kashe mutanen, ya ce sun shafe tsawon watanni suna ta’addanci a yankin ba tare da jami’an tsaro sun yi nasarar kama su ba.

“Sun mamaye yankinmu da yammacin jiya (Litinin), sun kashe mutanenmu, an kona wasu daga cikin wadanda abin ya shafa, ba za a iya gane su ba, yayin da ‘yan fashin dajin suka kona gidajensu.

Danlami ya kuma bayyana cewa a lokacin da ‘yan bindigar ke kashe wadanda abin ya shafa, maza da mata sun yi ta tururuwa domin tsira yayin da aka bar yara kanana.

LABARAI MASU NASABA

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

“Wannan abu ne mai ban tsoro da ban tausayi yayin da mutane kusan 8 suka kasa tsira daga ruwan harsashi daga ‘yan fashin dajin yayin da wasu da dama suka samu raunuka.”

“Rundunar ‘yan banga da ke yankin sun yi yunkurin yi wa ‘yan bindigar kofar rago sai dai karfin ‘yan bindigar ya fi karfinsu.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Taraba, DSP Usman Abubakar, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Usman ya kuma ce, bayanan da aka samu kan kashe-kashen sun nuna cewa maharan Fulani ne, ya ce “Kafin sojoji su zo wurin, sai da suka gudu daga yankin, ya ce ‘yan sanda sun mamayi maboyarsu domin kamo su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga
Labarai

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi
Manyan Labarai

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

November 8, 2025
Next Post
Kasar Sin Ta Samar Da Motoci Masu Amfani Da Wutar Lantarki Miliyan 20

Kasar Sin Ta Samar Da Motoci Masu Amfani Da Wutar Lantarki Miliyan 20

LABARAI MASU NASABA

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

November 8, 2025
Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

November 8, 2025
Kamfanoni Masu Jarin Waje Na Samun Kwarin Gwiwa Daga CIIE

Kamfanoni Masu Jarin Waje Na Samun Kwarin Gwiwa Daga CIIE

November 8, 2025
Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko

Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko

November 8, 2025
Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.