• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 4, Sun Raunata 5 A Kaduna

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Manyan Labarai
0
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 4, Sun Raunata 5 A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu da ake zargin ‘yan fashin daji ne sun mamayi kauyen anguwar Dandali da ke karamar hukumar Zariya a jihar Kaduna tare da kashe mutane hudu da jikkata wasu biyar.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin hakimin kauyen, Mallam Sunusi Yusuf, ya shaida cewar ‘yan bindigar sun isa kauyen ne da karfe misalin 10:30 na daren ranar Juma’a, inda suka fara harbi kan mai uwa da wabi.

  • Burina Kawo Ci Gaban Da Ba A Taba Tunani Ba A Harkar Fim —Ibrahim Ali (2)
  • Yadda Garkuwa Da Dalibai Ke Haifar Da Koma-baya Ga Ci Gaban Ilimi A Arewa

Ya yi bayanin cewa ‘yan bindigar sun samu nasarar harbe mutum tara gami da yin garkuwa da mutane biyar kafin daga bisani jami’an tsaro suka mamaye su wanda hakan ya janyo suka musayar wuta.

Ko da yake a cewarsa, duk da zuwan jami’an tsaron hakan bai hana ‘yan bindigar yin garkuwa da wasu ba.

“Daga cikin mutum tara da suka harba, hudu nan take suka mutu, yayin da kuma biyar suka samu raunuka.”

Labarai Masu Nasaba

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Wadanda aka kashe sun hada da Dahiru Tsalha Wawo, Bashir Salisu, Umar Yahuza da kuma Umar Bako. Sannan kuma wadanda suka jikkata su ne; Abubakar Yahuza, Bala Shamaki, Aliyu Ahmed, da Abdullahi Mamuda.

An birne wadanda suka rasa rayukansu a makabartar Hayin Dogo, Unguwar Dankali kamar yadda addinin musulunci ya tanadar.

Liman Alhaji Musa Tanko, mai unguwa ne a yankin, ya shaida cewa, al’umma suna cikin firgici da tashin hankali sakamakon yawaitar farmakin da ‘yan bindiga.

“Da farko da ‘yan bindigar na yawan kai hare-hare ne a kauyen Anguwar Dankali, amma yanzu suna mamayar makwafta Wusasa da yankin Kuregu wadanda ‘yan bindiga ke cigaba da kai hare-harensu. Wannan lamarin ya zama abun tashin hankali matuka yayin da ‘yan bindigan ke kara fadada aikace-aikacensu zuwa wasu yankunan,” ya shaida.

Tanko ya yi kiran a dukufa da addu’a domin neman kawo karshen matsalolin tsaro da suke faruwa a yankin.

A lokacin da aka tuntubi kakakin rundunar ‘yansandan jihar na rikon kwarya, ASP Mansir Hassan, ya yi alkawarin cewa zai tuntubi babban baturen dan sandan yankin, Dan Magaji kuma zai kira daga baya domin bayar da cikakken bayani kan abin da ya faru, amma har zuwa hada wannan rahoto bai kira ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HariKadunaKisaYan bindigaZariya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Burina Kawo Ci Gaban Da Ba A Taba Tunani Ba A Harkar Fim —Ibrahim Ali (2)

Next Post

Mutane Miliyan 826 Sun Yi Yawon Shakatawa A Yayin Ranaikun Hutu Na Kasar Sin

Related

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

6 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

12 hours ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

16 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

1 day ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

2 days ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

2 days ago
Next Post
Kasar sin

Mutane Miliyan 826 Sun Yi Yawon Shakatawa A Yayin Ranaikun Hutu Na Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.