• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 29 A Kauyen Abuja

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 29 A Kauyen Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masu garkuwa da mutane sun yi awon gaba da wasu mutane 29 da suka hada da manya maza, matan aure da yara a kauyen Yewuti, mahaifar tsohon mataimakin shugaban karamar hukumar Kwali, Alhaji Zubairu Jibrin Yewuti.

An samu labarin cewa wasu matan aure biyu, Zainab Umar da Aisha Zubairu, sun tsere daga hannun wadanda suka yi garkuwa da su a lokacin da aka kai su cikin daji.

  • Lardunan Sin 8 Sun Samu Karuwar GDP Da Kaso Sama Da 5 Bisa Dari A Rubu’in Farkon Bana
  • Yanzu-yanzun: El-Rufai Ya Nada Sabbin Alkalai 15 Kasa Da Kwana 35 Ya Mika Mulki

Daga cikin wadanda aka sace akwai Idris Mohammed, Abdullahi Zubairu, Sani S. Magani, Peter Modu, Ibrahim Mamman, Yellow Abdulrasheed, Musa Suleiman, Simbiya Ishaku, Sumaiya Ibrahim, Muktari Yunusa da Mohammed Yeluwa da Rahmat Shagari.

Sauran wadanda abin ya shafa sun hada da, Sumaiya Abubakar Yelwa, Mohammed Yelwa, Maimuna Muhammad, Hussaini Ya Nda Agyana, Hamza Ibrahim, Lantana Yunusa, Nabila Agyana, Rufai Salihu, Nafisa Aminu, Kasimu Adamu, Abako Adamu, Abdulyakin Aliyu, Lukman Aliyu, Rahina Audu, Abdulrazak Usman, Sadiya Usman, Darius Samuel da Japheth Osu.

Wani mazaunin garin Yewuti, wanda ya tsere, Shuaibu Ndako, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin a lokacin da wakilinmu ya ziyarci yankin a ranar Talata, ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 1 na daren ranar Talata, inda masu garkuwa da mutane da yawa suka mamaye al’ummar.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

Ya ce masu garkuwa da mutanen da suka raba kan su rukuni-rukuni, sun je gidaje takwas ne a yayin da suke ta harbe-harbe, inda suka tafi da mazauna yankin ciki har da yara da matan aure cikin daji.

“Allah ne ya cece ni. Da na fara jin an buga min kofa, na leko ta taga na ga masu garkuwa da mutane ne. Don haka na buya,” in ji shi.

Ya ce an yi garkuwa da yara biyu da mata biyu a gidansa kafin masu garkuwan su wuce gida na gaba bayan sun bude kofar gidan ta karfin tsiya.

Mataimakin shugaban karamar hukumar, Alhaji Zubairu Jibrin Yewuti, wanda ya zanta da wakilinmu a kauyen, ya ce an yi garkuwa da kaninsa Idris da matan yayansa guda biyu da wani yaro a gidansu.

Ya ce masu garkuwa da mutanen da suka yi aiki daga karfe 1 na dare zuwa karfe 3 na dare, sun mamaye gidaje sama da takwas sannan suka yi awon gaba da mutane 29 da suka hada da mata da maza da yara.

Ya ce wasu matan aure biyu sun yi nasarar tserewa daga hannun wadanda suka sace su yayin da aka kai su da sauran wadanda abin ya shafa cikin daji.

Shi ma Etsu Abawa na Yewuti, Alhaji Isyaku Yakubu Yewuti, ya tabbatar da cewa an yi awon gaba da mutanensa 29.

Ya ce an kai mutane biyu da suka samu raunukan harbin bindiga zuwa wani asibiti mai zaman kansa da ke Kwali.

Sarkin wanda ya ce daukacin al’ummar yankin sun firgita da harbin bindiga da masu garkuwa da mutanen ke yi a lokaci-lokaci, ya kuma yi kira ga jami’an tsaro da abin ya shafa da su taimaka masa wajen ceto wadanda aka sace.

Mutanen kauyen Awawa da ke makwabtaka da garin Abaji da Wako suka shiga cikin jama’a don jajantawa iyalan wadanda aka sace.

An kuma ga mafarauta, ‘yan banga, da ‘yan sanda a cikin motocin kirar Hilux guda uku suna shawagi a dajin kauyen.

Kawo yanzu dai babu wani martani a hukumance daga kakakin rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja, DSP Adeh Josephine, kan sabon harin da aka yi na garkuwa da mutane har zuwa lokacin hada rahoton.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Garkuwa Da MutaneHariKauyen AbujaYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Lardunan Sin 8 Sun Samu Karuwar GDP Da Kaso Sama Da 5 Bisa Dari A Rubu’in Farkon Bana

Next Post

Hatsarin Mota Ya Yi Ajalin ‘Yansanda 3 A Kaduna

Related

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

3 hours ago
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

4 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
Manyan Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

18 hours ago
Wata Mata Ta Kashe Dan Hayar Da Ke Gidanta A Ondo
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

21 hours ago
Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027
Siyasa

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

1 day ago
Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19
Manyan Labarai

Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

1 day ago
Next Post
Hatsarin Mota Ya Yi Ajalin ‘Yansanda 3 A Kaduna

Hatsarin Mota Ya Yi Ajalin 'Yansanda 3 A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.