• English
  • Business News
Wednesday, July 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 29 A Kauyen Abuja

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 29 A Kauyen Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masu garkuwa da mutane sun yi awon gaba da wasu mutane 29 da suka hada da manya maza, matan aure da yara a kauyen Yewuti, mahaifar tsohon mataimakin shugaban karamar hukumar Kwali, Alhaji Zubairu Jibrin Yewuti.

An samu labarin cewa wasu matan aure biyu, Zainab Umar da Aisha Zubairu, sun tsere daga hannun wadanda suka yi garkuwa da su a lokacin da aka kai su cikin daji.

  • Lardunan Sin 8 Sun Samu Karuwar GDP Da Kaso Sama Da 5 Bisa Dari A Rubu’in Farkon Bana
  • Yanzu-yanzun: El-Rufai Ya Nada Sabbin Alkalai 15 Kasa Da Kwana 35 Ya Mika Mulki

Daga cikin wadanda aka sace akwai Idris Mohammed, Abdullahi Zubairu, Sani S. Magani, Peter Modu, Ibrahim Mamman, Yellow Abdulrasheed, Musa Suleiman, Simbiya Ishaku, Sumaiya Ibrahim, Muktari Yunusa da Mohammed Yeluwa da Rahmat Shagari.

Sauran wadanda abin ya shafa sun hada da, Sumaiya Abubakar Yelwa, Mohammed Yelwa, Maimuna Muhammad, Hussaini Ya Nda Agyana, Hamza Ibrahim, Lantana Yunusa, Nabila Agyana, Rufai Salihu, Nafisa Aminu, Kasimu Adamu, Abako Adamu, Abdulyakin Aliyu, Lukman Aliyu, Rahina Audu, Abdulrazak Usman, Sadiya Usman, Darius Samuel da Japheth Osu.

Wani mazaunin garin Yewuti, wanda ya tsere, Shuaibu Ndako, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin a lokacin da wakilinmu ya ziyarci yankin a ranar Talata, ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 1 na daren ranar Talata, inda masu garkuwa da mutane da yawa suka mamaye al’ummar.

Labarai Masu Nasaba

Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura

Da Ɗumi-Ɗumi: Shettima Ya Isa Katsina Da Gawar Buhari

Ya ce masu garkuwa da mutanen da suka raba kan su rukuni-rukuni, sun je gidaje takwas ne a yayin da suke ta harbe-harbe, inda suka tafi da mazauna yankin ciki har da yara da matan aure cikin daji.

“Allah ne ya cece ni. Da na fara jin an buga min kofa, na leko ta taga na ga masu garkuwa da mutane ne. Don haka na buya,” in ji shi.

Ya ce an yi garkuwa da yara biyu da mata biyu a gidansa kafin masu garkuwan su wuce gida na gaba bayan sun bude kofar gidan ta karfin tsiya.

Mataimakin shugaban karamar hukumar, Alhaji Zubairu Jibrin Yewuti, wanda ya zanta da wakilinmu a kauyen, ya ce an yi garkuwa da kaninsa Idris da matan yayansa guda biyu da wani yaro a gidansu.

Ya ce masu garkuwa da mutanen da suka yi aiki daga karfe 1 na dare zuwa karfe 3 na dare, sun mamaye gidaje sama da takwas sannan suka yi awon gaba da mutane 29 da suka hada da mata da maza da yara.

Ya ce wasu matan aure biyu sun yi nasarar tserewa daga hannun wadanda suka sace su yayin da aka kai su da sauran wadanda abin ya shafa cikin daji.

Shi ma Etsu Abawa na Yewuti, Alhaji Isyaku Yakubu Yewuti, ya tabbatar da cewa an yi awon gaba da mutanensa 29.

Ya ce an kai mutane biyu da suka samu raunukan harbin bindiga zuwa wani asibiti mai zaman kansa da ke Kwali.

Sarkin wanda ya ce daukacin al’ummar yankin sun firgita da harbin bindiga da masu garkuwa da mutanen ke yi a lokaci-lokaci, ya kuma yi kira ga jami’an tsaro da abin ya shafa da su taimaka masa wajen ceto wadanda aka sace.

Mutanen kauyen Awawa da ke makwabtaka da garin Abaji da Wako suka shiga cikin jama’a don jajantawa iyalan wadanda aka sace.

An kuma ga mafarauta, ‘yan banga, da ‘yan sanda a cikin motocin kirar Hilux guda uku suna shawagi a dajin kauyen.

Kawo yanzu dai babu wani martani a hukumance daga kakakin rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja, DSP Adeh Josephine, kan sabon harin da aka yi na garkuwa da mutane har zuwa lokacin hada rahoton.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Garkuwa Da MutaneHariKauyen AbujaYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Lardunan Sin 8 Sun Samu Karuwar GDP Da Kaso Sama Da 5 Bisa Dari A Rubu’in Farkon Bana

Next Post

Hatsarin Mota Ya Yi Ajalin ‘Yansanda 3 A Kaduna

Related

Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura
Manyan Labarai

Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura

11 hours ago
Da Ɗumi-Ɗumi: Shettima Ya Isa Katsina Da Gawar Buhari
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-Ɗumi: Shettima Ya Isa Katsina Da Gawar Buhari

12 hours ago
Tinubu Ya Isa Katsina Don Tarbar Gawar Buhari
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Katsina Don Tarbar Gawar Buhari

12 hours ago
Buhari Na Cikin Ƙoshin Lafiya Kwana Ɗaya Kafin Rasuwarsa – Mamman Daura
Manyan Labarai

Buhari Na Cikin Ƙoshin Lafiya Kwana Ɗaya Kafin Rasuwarsa – Mamman Daura

12 hours ago
Buhari Da Ya Daɗe Da Rasuwa Idan A Asibitocin Nijeriya Ake Duba Shi – Adesina
Manyan Labarai

Buhari Da Ya Daɗe Da Rasuwa Idan A Asibitocin Nijeriya Ake Duba Shi – Adesina

14 hours ago
HOTUNA: An Tsaurara Tsaro A Gidan Buhari Da Ke Daura
Hotuna

HOTUNA: An Tsaurara Tsaro A Gidan Buhari Da Ke Daura

15 hours ago
Next Post
Hatsarin Mota Ya Yi Ajalin ‘Yansanda 3 A Kaduna

Hatsarin Mota Ya Yi Ajalin 'Yansanda 3 A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

July 15, 2025
Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

July 15, 2025
VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

July 15, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

July 15, 2025
An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

July 15, 2025
Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

July 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

July 15, 2025
Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

July 15, 2025
Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

July 15, 2025
Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

July 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.