• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindigan Da Ake Fatattaka Daga Arewa Maso Yamma Na Kwararowa Arewa Maso Gabas – Gwamnoni

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Gwamnonin Arewa Maso Gabas Za Su Samar Da Kamfanin Zirga-zirgan Jirgin Sama
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Gwamnonin Arewa Maso Gabas ta nuna damuwarta kan yadda ‘yan bindigan da jami’an tsaro ke fatattaka daga shiyyar Arewa Maso Yamma ke kwararowa zuwa shiyyar. 

Gwamnonin suna masu cewa ana samun nasara sosai wajen kyautata harkokin tsaro a shiyyar, amma suna fuskantar barazanar yawaitar shigowar ‘yan bindiga da jami’ar tsaro ke fatattakar ga Arewa Maso Yamma.

  • An Yi Ta Barazanar Kashe Ni Kan Shaidar Katin Dan Kasa Da Rijistar Layuka – Pantami
  • Ba A Kashe Dansanda A Harin Da Mahara Suka Kai Ebonyi Ba – ‘Yansanda

A jawabin bayan taron da kungiyar gwamonin Arewa Maso Gabas (NSGF) ta fitar wadda Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni ya karanta wa ‘yan jarida a ranar Juma’a sun yi kira da a hada karfi da karfe da hukumomin tsaro da Gwamnatin tarayya domin dakile wannan matsalar.

Gwamnonin Arewa Maso Gabas din da suka hada da Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri; Bauchi, Bala Muhammad; Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum (Shugaban kungiyar NEGF); Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya; Taraba Darius Dickson Ishaku, da jihar Yobe, Mai Mala Buni sun cimma wannan matsayar ne a lokacin taron su karo na bakwai da ya gudana a jihar Gombe.

Kungiyar ta nuna farin cikinta dangane da aikin hadin guiwa da ake samu tsakanin Gwamnonin jihohin shida wadda sakamakon hakan ana samun cimma muhimman nasarori na kyautata rayuwar al’ummar jihohin.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

Gwamnonin sun jinjina wa shugaban kasa Muhammadu Buhari a bisa kokarinsa wajen yaki da matsalar Boko Haram, tare da sa’ayinsa na kyautata harkokin tsaro a shiyyar wadda zuwa yanzu a cewarsu an samu nasarori.

Kungiyar ta ce, raguwar fada tsakanin manoma da Fulani makiyaya abun sha’awa ne.

Kungiyar ta yi kira ga Gwamnatin tarayya da ta kara azama wajen fatattakar ‘yan garkuwa da mutane da suka addabi wasu sassan kasar nan.

Kungiyar ta nuna damuwarta dangane da karancin samun wutar lantarki a shiyyar Arewa Maso Gabas tare da yin kira da a shawo kan matsalar.

Kan matsalar na wutar lantarki, Gwamnonin sun yi kira ga Gwamnatin tarayya da ta gaggauta gudanar da aikin samar da wutar lantarki Manbila.

Gwamnonin sun yi nuni da bukatar yin amfani da dimbin albarkatun da ba a yi amfani da su a yankin ba, ta hanyar inganta hada-hadar kasuwanci tare da gudanar da baje kolin kasuwanci da nufin jawo hankalin kasashen waje wajen zuba hannun jari.

Don haka, kungiyar ta bukaci Majalisar ’Yan Kasuwa ta Arewa-maso-Gabas da ta farfado da kasuwar hada-hadar kasuwanci ta Arewa Maso Gabas da kasuwannin kayyayaki don bunkasar da harkokin tattalin arziki.

Kazalika, taron ya jinjina wa Gwamnatin tarayya wajen kafa Jami’ar Kimiyyar lafiya a garin Azare da zimmar shawo kan tulin matsalolin da suke sashin kiwon lafiya, sun kuma yi alkawarin taimaka wa Jami’ar domin cimma manufar da aka samar da ita.

Kungiyar Gwamnonin Arewa sun nuna matukar damuwarsu dangane da ambaliyar ruwa da ta barnata da lalata gidaje, gonakai da gine-ginen jama’a da dama.

Sun nemi Gwamnatin tarayya cikin gaggawa da ta umarci hukumomin da abun ya shafa da su tunkari yankunan da ambaliyar ta shafa domin kai agajin da ya kamata.

Daga karshe sun jinjina wa gwamnan Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya bisa amsar bakwancin taron, tare da cewa taron nan gaba na kungiyar (karo na 8) da za su yi a ranar Juma’a 25 ga watan Nuwamba zai gudana ne a Maiduguri ta jihar Borno.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BarazanaDamuwaKungiyar GwamnoniTaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Ta Barazanar Kashe Ni Kan Shaidar Katin Dan Kasa Da Rijistar Layuka – Pantami

Next Post

Ganduje Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Usman Bala

Related

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

2 minutes ago
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana
Labarai

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

2 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

3 hours ago
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

11 hours ago
Tinubu
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

12 hours ago
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa
Labarai

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

13 hours ago
Next Post
Ganduje Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Usman Bala

Ganduje Ya Yi Ta'aziyyar Rasuwar Mahaifin Usman Bala

LABARAI MASU NASABA

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.