ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindigan Da Ake Fatattaka Daga Arewa Maso Yamma Na Kwararowa Arewa Maso Gabas – Gwamnoni

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Gwamnoni

Kungiyar Gwamnonin Arewa Maso Gabas ta nuna damuwarta kan yadda ‘yan bindigan da jami’an tsaro ke fatattaka daga shiyyar Arewa Maso Yamma ke kwararowa zuwa shiyyar. 

Gwamnonin suna masu cewa ana samun nasara sosai wajen kyautata harkokin tsaro a shiyyar, amma suna fuskantar barazanar yawaitar shigowar ‘yan bindiga da jami’ar tsaro ke fatattakar ga Arewa Maso Yamma.

  • An Yi Ta Barazanar Kashe Ni Kan Shaidar Katin Dan Kasa Da Rijistar Layuka – Pantami
  • Ba A Kashe Dansanda A Harin Da Mahara Suka Kai Ebonyi Ba – ‘Yansanda

A jawabin bayan taron da kungiyar gwamonin Arewa Maso Gabas (NSGF) ta fitar wadda Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni ya karanta wa ‘yan jarida a ranar Juma’a sun yi kira da a hada karfi da karfe da hukumomin tsaro da Gwamnatin tarayya domin dakile wannan matsalar.

ADVERTISEMENT

Gwamnonin Arewa Maso Gabas din da suka hada da Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri; Bauchi, Bala Muhammad; Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum (Shugaban kungiyar NEGF); Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya; Taraba Darius Dickson Ishaku, da jihar Yobe, Mai Mala Buni sun cimma wannan matsayar ne a lokacin taron su karo na bakwai da ya gudana a jihar Gombe.

Kungiyar ta nuna farin cikinta dangane da aikin hadin guiwa da ake samu tsakanin Gwamnonin jihohin shida wadda sakamakon hakan ana samun cimma muhimman nasarori na kyautata rayuwar al’ummar jihohin.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Gwamnonin sun jinjina wa shugaban kasa Muhammadu Buhari a bisa kokarinsa wajen yaki da matsalar Boko Haram, tare da sa’ayinsa na kyautata harkokin tsaro a shiyyar wadda zuwa yanzu a cewarsu an samu nasarori.

Kungiyar ta ce, raguwar fada tsakanin manoma da Fulani makiyaya abun sha’awa ne.

Kungiyar ta yi kira ga Gwamnatin tarayya da ta kara azama wajen fatattakar ‘yan garkuwa da mutane da suka addabi wasu sassan kasar nan.

Kungiyar ta nuna damuwarta dangane da karancin samun wutar lantarki a shiyyar Arewa Maso Gabas tare da yin kira da a shawo kan matsalar.

Kan matsalar na wutar lantarki, Gwamnonin sun yi kira ga Gwamnatin tarayya da ta gaggauta gudanar da aikin samar da wutar lantarki Manbila.

Gwamnonin sun yi nuni da bukatar yin amfani da dimbin albarkatun da ba a yi amfani da su a yankin ba, ta hanyar inganta hada-hadar kasuwanci tare da gudanar da baje kolin kasuwanci da nufin jawo hankalin kasashen waje wajen zuba hannun jari.

Don haka, kungiyar ta bukaci Majalisar ’Yan Kasuwa ta Arewa-maso-Gabas da ta farfado da kasuwar hada-hadar kasuwanci ta Arewa Maso Gabas da kasuwannin kayyayaki don bunkasar da harkokin tattalin arziki.

Kazalika, taron ya jinjina wa Gwamnatin tarayya wajen kafa Jami’ar Kimiyyar lafiya a garin Azare da zimmar shawo kan tulin matsalolin da suke sashin kiwon lafiya, sun kuma yi alkawarin taimaka wa Jami’ar domin cimma manufar da aka samar da ita.

Kungiyar Gwamnonin Arewa sun nuna matukar damuwarsu dangane da ambaliyar ruwa da ta barnata da lalata gidaje, gonakai da gine-ginen jama’a da dama.

Sun nemi Gwamnatin tarayya cikin gaggawa da ta umarci hukumomin da abun ya shafa da su tunkari yankunan da ambaliyar ta shafa domin kai agajin da ya kamata.

Daga karshe sun jinjina wa gwamnan Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya bisa amsar bakwancin taron, tare da cewa taron nan gaba na kungiyar (karo na 8) da za su yi a ranar Juma’a 25 ga watan Nuwamba zai gudana ne a Maiduguri ta jihar Borno.

Gwamnoni
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Ganduje Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Usman Bala

Ganduje Ya Yi Ta'aziyyar Rasuwar Mahaifin Usman Bala

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.