ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindigan Da Ake Fatattaka Daga Arewa Maso Yamma Na Kwararowa Arewa Maso Gabas – Gwamnoni

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Gwamnoni

Kungiyar Gwamnonin Arewa Maso Gabas ta nuna damuwarta kan yadda ‘yan bindigan da jami’an tsaro ke fatattaka daga shiyyar Arewa Maso Yamma ke kwararowa zuwa shiyyar. 

Gwamnonin suna masu cewa ana samun nasara sosai wajen kyautata harkokin tsaro a shiyyar, amma suna fuskantar barazanar yawaitar shigowar ‘yan bindiga da jami’ar tsaro ke fatattakar ga Arewa Maso Yamma.

  • An Yi Ta Barazanar Kashe Ni Kan Shaidar Katin Dan Kasa Da Rijistar Layuka – Pantami
  • Ba A Kashe Dansanda A Harin Da Mahara Suka Kai Ebonyi Ba – ‘Yansanda

A jawabin bayan taron da kungiyar gwamonin Arewa Maso Gabas (NSGF) ta fitar wadda Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni ya karanta wa ‘yan jarida a ranar Juma’a sun yi kira da a hada karfi da karfe da hukumomin tsaro da Gwamnatin tarayya domin dakile wannan matsalar.

ADVERTISEMENT

Gwamnonin Arewa Maso Gabas din da suka hada da Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri; Bauchi, Bala Muhammad; Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum (Shugaban kungiyar NEGF); Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya; Taraba Darius Dickson Ishaku, da jihar Yobe, Mai Mala Buni sun cimma wannan matsayar ne a lokacin taron su karo na bakwai da ya gudana a jihar Gombe.

Kungiyar ta nuna farin cikinta dangane da aikin hadin guiwa da ake samu tsakanin Gwamnonin jihohin shida wadda sakamakon hakan ana samun cimma muhimman nasarori na kyautata rayuwar al’ummar jihohin.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnonin sun jinjina wa shugaban kasa Muhammadu Buhari a bisa kokarinsa wajen yaki da matsalar Boko Haram, tare da sa’ayinsa na kyautata harkokin tsaro a shiyyar wadda zuwa yanzu a cewarsu an samu nasarori.

Kungiyar ta ce, raguwar fada tsakanin manoma da Fulani makiyaya abun sha’awa ne.

Kungiyar ta yi kira ga Gwamnatin tarayya da ta kara azama wajen fatattakar ‘yan garkuwa da mutane da suka addabi wasu sassan kasar nan.

Kungiyar ta nuna damuwarta dangane da karancin samun wutar lantarki a shiyyar Arewa Maso Gabas tare da yin kira da a shawo kan matsalar.

Kan matsalar na wutar lantarki, Gwamnonin sun yi kira ga Gwamnatin tarayya da ta gaggauta gudanar da aikin samar da wutar lantarki Manbila.

Gwamnonin sun yi nuni da bukatar yin amfani da dimbin albarkatun da ba a yi amfani da su a yankin ba, ta hanyar inganta hada-hadar kasuwanci tare da gudanar da baje kolin kasuwanci da nufin jawo hankalin kasashen waje wajen zuba hannun jari.

Don haka, kungiyar ta bukaci Majalisar ’Yan Kasuwa ta Arewa-maso-Gabas da ta farfado da kasuwar hada-hadar kasuwanci ta Arewa Maso Gabas da kasuwannin kayyayaki don bunkasar da harkokin tattalin arziki.

Kazalika, taron ya jinjina wa Gwamnatin tarayya wajen kafa Jami’ar Kimiyyar lafiya a garin Azare da zimmar shawo kan tulin matsalolin da suke sashin kiwon lafiya, sun kuma yi alkawarin taimaka wa Jami’ar domin cimma manufar da aka samar da ita.

Kungiyar Gwamnonin Arewa sun nuna matukar damuwarsu dangane da ambaliyar ruwa da ta barnata da lalata gidaje, gonakai da gine-ginen jama’a da dama.

Sun nemi Gwamnatin tarayya cikin gaggawa da ta umarci hukumomin da abun ya shafa da su tunkari yankunan da ambaliyar ta shafa domin kai agajin da ya kamata.

Daga karshe sun jinjina wa gwamnan Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya bisa amsar bakwancin taron, tare da cewa taron nan gaba na kungiyar (karo na 8) da za su yi a ranar Juma’a 25 ga watan Nuwamba zai gudana ne a Maiduguri ta jihar Borno.

Gwamnoni
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Ganduje Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Usman Bala

Ganduje Ya Yi Ta'aziyyar Rasuwar Mahaifin Usman Bala

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.