• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

’Yan Fashi Sun Yi Shigar Injiniyoyi, Sun Saci Manyan Na’urorin Sadarwa

by Sabo Ahmad
2 years ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
'Yan fashi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yan sandan Jihar Akwa Ibom a ranar Asabar din da ta gabata ta cafke wasu mutum uku da ake zargi da aikata barna a kamfanin sadarwa, ta hanyar yin shigar injiniyoyin don satar batir na kamfanonin sadarwa a jihar.

Da yake jawabi ga manema labarai a shelkwatar rundunar, Uyo, babban birnin jihar yayin da yake gabatar da wadanda ake zargin, kwamishinan ‘yansandan jihar, Olatoye Durosinmi, ya ce an samu nasarar kwato wasu batura guda shida na ‘mast backup’ da wata mota kirar Toyota Camry da aka yi amfani da su wajen aikata laifin.

  • Tataburzar Hana Shigo Da Taliyar ‘Yan Yara Daga Waje Za Ta Zama Alheri Ga Nijeriya

Kwamishinan ‘yansandan, wanda ya ce an kama su ne a ranar 21 ga Maris, 2023, ta hannun rundunar ‘yan sandan Eagle Response Skuad, bayan samun sahihan bayanai, ya sanya sunayen wadanda ake zargin sun hada da Chinwe Nwabara, Bright Godswill da Chinedu Nweke.

A cewarsa, wadanda ake zargin wadanda suka yi basaja da injiniyoyi sun tuka mota kirar Toyota Camry mai launin toka mai lamba KJA 321 FS tare da sace kayan aikin da kudinsu ya haura Naira miliyan 1.6 kafin a kama su.

Durosinmi ya ce, “A ranar 21 ga Maris, 2023, da misalin karfe 5 na yamma, bisa wani ingantaccen rahoto da aka samu cewa ‘yan bindigar da suka yi basaja a matsayin injiniyoyi, sun tuka mota kirar Toyota Camry mai launin toka mai lamba KJA 321 FS, a kewayen Uyo, Abak, Oron da Okobo, sun lalata su tare da satar batir na baya-bayan nan na kamfanonin sadarwa da darajarsu ta kai Naira miliyan 1.6, wani dogon bincike da jami’an Eagle Response Skuad na rundunar ‘yan sandan ya yi ya kai ga cafke wasu mutane uku da ake zargi da suka hada da Chinwe Nwabara, Bright Godswill da Chinedu Nweke.

Labarai Masu Nasaba

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

Ya ce an kuma kama wasu mutum hudu da suka yi garkuwa da wani babban sakatare na jihar Ignatius Brown na Karamar Hukumar Abak tare da neman kudin fansa Naira miliyan 80.

Ya ce ’yan uwa saboda bacin rai ne suka tattara wasu kudade suka biya wadanda ake zargin amma jami’an ‘yansanda sun samu nasarar gano maboyar barayin, inda suka ceto wanda aka sace tare da cafke wasu da ake zargi.

Ya ce an samu nasarar kwato bindigar gida guda daya da bindigu na katako guda uku daga hannun wadanda ake zargin.

A halin da ake ciki, daya daga cikin wadanda ake zargin, Sunday Ekwere, ya amsa laifin karbar Naira 850,000 daga kudin fansa da suka karba.sabo


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ba Shi Da Ikon Tsayar Da Wanda Zai Zama Shugaban Majalisa —Yari

Next Post

An Gayyaci CMG Don Ya Zama Babbar Kafar Yada Labarai Kan Gasar Olympics Ta Paris

Related

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

3 weeks ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

3 weeks ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

3 weeks ago
An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

4 weeks ago
Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara
Kotu Da Ɗansanda

Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara

4 weeks ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi Tare Da Kwato Makamai A Delta

4 weeks ago
Next Post
An Gayyaci CMG Don Ya Zama Babbar Kafar Yada Labarai Kan Gasar Olympics Ta Paris

An Gayyaci CMG Don Ya Zama Babbar Kafar Yada Labarai Kan Gasar Olympics Ta Paris

LABARAI MASU NASABA

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.