• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

’Yan Fashi Sun Yi Shigar Injiniyoyi, Sun Saci Manyan Na’urorin Sadarwa

by Sabo Ahmad
2 years ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
'Yan fashi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yan sandan Jihar Akwa Ibom a ranar Asabar din da ta gabata ta cafke wasu mutum uku da ake zargi da aikata barna a kamfanin sadarwa, ta hanyar yin shigar injiniyoyin don satar batir na kamfanonin sadarwa a jihar.

Da yake jawabi ga manema labarai a shelkwatar rundunar, Uyo, babban birnin jihar yayin da yake gabatar da wadanda ake zargin, kwamishinan ‘yansandan jihar, Olatoye Durosinmi, ya ce an samu nasarar kwato wasu batura guda shida na ‘mast backup’ da wata mota kirar Toyota Camry da aka yi amfani da su wajen aikata laifin.

  • Tataburzar Hana Shigo Da Taliyar ‘Yan Yara Daga Waje Za Ta Zama Alheri Ga Nijeriya

Kwamishinan ‘yansandan, wanda ya ce an kama su ne a ranar 21 ga Maris, 2023, ta hannun rundunar ‘yan sandan Eagle Response Skuad, bayan samun sahihan bayanai, ya sanya sunayen wadanda ake zargin sun hada da Chinwe Nwabara, Bright Godswill da Chinedu Nweke.

A cewarsa, wadanda ake zargin wadanda suka yi basaja da injiniyoyi sun tuka mota kirar Toyota Camry mai launin toka mai lamba KJA 321 FS tare da sace kayan aikin da kudinsu ya haura Naira miliyan 1.6 kafin a kama su.

Durosinmi ya ce, “A ranar 21 ga Maris, 2023, da misalin karfe 5 na yamma, bisa wani ingantaccen rahoto da aka samu cewa ‘yan bindigar da suka yi basaja a matsayin injiniyoyi, sun tuka mota kirar Toyota Camry mai launin toka mai lamba KJA 321 FS, a kewayen Uyo, Abak, Oron da Okobo, sun lalata su tare da satar batir na baya-bayan nan na kamfanonin sadarwa da darajarsu ta kai Naira miliyan 1.6, wani dogon bincike da jami’an Eagle Response Skuad na rundunar ‘yan sandan ya yi ya kai ga cafke wasu mutane uku da ake zargi da suka hada da Chinwe Nwabara, Bright Godswill da Chinedu Nweke.

Labarai Masu Nasaba

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

Ya ce an kuma kama wasu mutum hudu da suka yi garkuwa da wani babban sakatare na jihar Ignatius Brown na Karamar Hukumar Abak tare da neman kudin fansa Naira miliyan 80.

Ya ce ’yan uwa saboda bacin rai ne suka tattara wasu kudade suka biya wadanda ake zargin amma jami’an ‘yansanda sun samu nasarar gano maboyar barayin, inda suka ceto wanda aka sace tare da cafke wasu da ake zargi.

Ya ce an samu nasarar kwato bindigar gida guda daya da bindigu na katako guda uku daga hannun wadanda ake zargin.

A halin da ake ciki, daya daga cikin wadanda ake zargin, Sunday Ekwere, ya amsa laifin karbar Naira 850,000 daga kudin fansa da suka karba.sabo


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ba Shi Da Ikon Tsayar Da Wanda Zai Zama Shugaban Majalisa —Yari

Next Post

An Gayyaci CMG Don Ya Zama Babbar Kafar Yada Labarai Kan Gasar Olympics Ta Paris

Related

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

1 day ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

1 day ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

2 days ago
An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

1 week ago
Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara
Kotu Da Ɗansanda

Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara

1 week ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi Tare Da Kwato Makamai A Delta

1 week ago
Next Post
An Gayyaci CMG Don Ya Zama Babbar Kafar Yada Labarai Kan Gasar Olympics Ta Paris

An Gayyaci CMG Don Ya Zama Babbar Kafar Yada Labarai Kan Gasar Olympics Ta Paris

LABARAI MASU NASABA

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.