• English
  • Business News
Thursday, May 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

’Yan Fashi Sun Yi Shigar Injiniyoyi, Sun Saci Manyan Na’urorin Sadarwa

by Sabo Ahmad
2 years ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
'Yan fashi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yan sandan Jihar Akwa Ibom a ranar Asabar din da ta gabata ta cafke wasu mutum uku da ake zargi da aikata barna a kamfanin sadarwa, ta hanyar yin shigar injiniyoyin don satar batir na kamfanonin sadarwa a jihar.

Da yake jawabi ga manema labarai a shelkwatar rundunar, Uyo, babban birnin jihar yayin da yake gabatar da wadanda ake zargin, kwamishinan ‘yansandan jihar, Olatoye Durosinmi, ya ce an samu nasarar kwato wasu batura guda shida na ‘mast backup’ da wata mota kirar Toyota Camry da aka yi amfani da su wajen aikata laifin.

  • Tataburzar Hana Shigo Da Taliyar ‘Yan Yara Daga Waje Za Ta Zama Alheri Ga Nijeriya

Kwamishinan ‘yansandan, wanda ya ce an kama su ne a ranar 21 ga Maris, 2023, ta hannun rundunar ‘yan sandan Eagle Response Skuad, bayan samun sahihan bayanai, ya sanya sunayen wadanda ake zargin sun hada da Chinwe Nwabara, Bright Godswill da Chinedu Nweke.

A cewarsa, wadanda ake zargin wadanda suka yi basaja da injiniyoyi sun tuka mota kirar Toyota Camry mai launin toka mai lamba KJA 321 FS tare da sace kayan aikin da kudinsu ya haura Naira miliyan 1.6 kafin a kama su.

Durosinmi ya ce, “A ranar 21 ga Maris, 2023, da misalin karfe 5 na yamma, bisa wani ingantaccen rahoto da aka samu cewa ‘yan bindigar da suka yi basaja a matsayin injiniyoyi, sun tuka mota kirar Toyota Camry mai launin toka mai lamba KJA 321 FS, a kewayen Uyo, Abak, Oron da Okobo, sun lalata su tare da satar batir na baya-bayan nan na kamfanonin sadarwa da darajarsu ta kai Naira miliyan 1.6, wani dogon bincike da jami’an Eagle Response Skuad na rundunar ‘yan sandan ya yi ya kai ga cafke wasu mutane uku da ake zargi da suka hada da Chinwe Nwabara, Bright Godswill da Chinedu Nweke.

Labarai Masu Nasaba

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

Ya ce an kuma kama wasu mutum hudu da suka yi garkuwa da wani babban sakatare na jihar Ignatius Brown na Karamar Hukumar Abak tare da neman kudin fansa Naira miliyan 80.

Ya ce ’yan uwa saboda bacin rai ne suka tattara wasu kudade suka biya wadanda ake zargin amma jami’an ‘yansanda sun samu nasarar gano maboyar barayin, inda suka ceto wanda aka sace tare da cafke wasu da ake zargi.

Ya ce an samu nasarar kwato bindigar gida guda daya da bindigu na katako guda uku daga hannun wadanda ake zargin.

A halin da ake ciki, daya daga cikin wadanda ake zargin, Sunday Ekwere, ya amsa laifin karbar Naira 850,000 daga kudin fansa da suka karba.sabo


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ba Shi Da Ikon Tsayar Da Wanda Zai Zama Shugaban Majalisa —Yari

Next Post

An Gayyaci CMG Don Ya Zama Babbar Kafar Yada Labarai Kan Gasar Olympics Ta Paris

Related

Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

1 month ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

3 months ago
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

3 months ago
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Na Farautar Wadanda Suka Kashe Dalibi A Katsina

3 months ago
Rikita-rikitar Da Ta Biyo Bayan Mutuwar Mawaki Mohbad
Kotu Da Ɗansanda

MohBad: Nurse Za Ta Fuskanci Shari’a, Sannan Kotu Ta Wanke Naira Marley, Sam Larry Da PrimeBoy

3 months ago
‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja

3 months ago
Next Post
An Gayyaci CMG Don Ya Zama Babbar Kafar Yada Labarai Kan Gasar Olympics Ta Paris

An Gayyaci CMG Don Ya Zama Babbar Kafar Yada Labarai Kan Gasar Olympics Ta Paris

LABARAI MASU NASABA

Darussan Koyi Daga Salon Bunkasa Kasa Na Sin

Darussan Koyi Daga Salon Bunkasa Kasa Na Sin

May 22, 2025
Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 

Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 

May 22, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Faransa

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Faransa

May 22, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

INEC Ta Samar Da Sashen Ƙirƙirarriyar Basira Domin Inganta Harkokin Zaɓe 

May 22, 2025
Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya

Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya

May 22, 2025
Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

May 22, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kashe Naira Tiriliyan 1.5 Don Magance Matsalar Abinci — Minista

Gwamnatin Tarayya Ta Kashe Naira Tiriliyan 1.5 Don Magance Matsalar Abinci — Minista

May 22, 2025
Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur

May 22, 2025
Trump Zai Shirya Liyafar Musamman Ga Manyan Ƴan Crypto 

Trump Zai Shirya Liyafar Musamman Ga Manyan Ƴan Crypto 

May 22, 2025
Tsaro Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Bunƙasa Tattalin Arziƙi – Atiku

Tsaro Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Bunƙasa Tattalin Arziƙi – Atiku

May 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.