ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

’Yan Fashi Sun Yi Shigar Injiniyoyi, Sun Saci Manyan Na’urorin Sadarwa

by Sabo Ahmad
3 years ago
'Yan fashi

Rundunar ‘yan sandan Jihar Akwa Ibom a ranar Asabar din da ta gabata ta cafke wasu mutum uku da ake zargi da aikata barna a kamfanin sadarwa, ta hanyar yin shigar injiniyoyin don satar batir na kamfanonin sadarwa a jihar.

Da yake jawabi ga manema labarai a shelkwatar rundunar, Uyo, babban birnin jihar yayin da yake gabatar da wadanda ake zargin, kwamishinan ‘yansandan jihar, Olatoye Durosinmi, ya ce an samu nasarar kwato wasu batura guda shida na ‘mast backup’ da wata mota kirar Toyota Camry da aka yi amfani da su wajen aikata laifin.

  • Tataburzar Hana Shigo Da Taliyar ‘Yan Yara Daga Waje Za Ta Zama Alheri Ga Nijeriya

Kwamishinan ‘yansandan, wanda ya ce an kama su ne a ranar 21 ga Maris, 2023, ta hannun rundunar ‘yan sandan Eagle Response Skuad, bayan samun sahihan bayanai, ya sanya sunayen wadanda ake zargin sun hada da Chinwe Nwabara, Bright Godswill da Chinedu Nweke.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, wadanda ake zargin wadanda suka yi basaja da injiniyoyi sun tuka mota kirar Toyota Camry mai launin toka mai lamba KJA 321 FS tare da sace kayan aikin da kudinsu ya haura Naira miliyan 1.6 kafin a kama su.

Durosinmi ya ce, “A ranar 21 ga Maris, 2023, da misalin karfe 5 na yamma, bisa wani ingantaccen rahoto da aka samu cewa ‘yan bindigar da suka yi basaja a matsayin injiniyoyi, sun tuka mota kirar Toyota Camry mai launin toka mai lamba KJA 321 FS, a kewayen Uyo, Abak, Oron da Okobo, sun lalata su tare da satar batir na baya-bayan nan na kamfanonin sadarwa da darajarsu ta kai Naira miliyan 1.6, wani dogon bincike da jami’an Eagle Response Skuad na rundunar ‘yan sandan ya yi ya kai ga cafke wasu mutane uku da ake zargi da suka hada da Chinwe Nwabara, Bright Godswill da Chinedu Nweke.

LABARAI MASU NASABA

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

Ya ce an kuma kama wasu mutum hudu da suka yi garkuwa da wani babban sakatare na jihar Ignatius Brown na Karamar Hukumar Abak tare da neman kudin fansa Naira miliyan 80.

Ya ce ’yan uwa saboda bacin rai ne suka tattara wasu kudade suka biya wadanda ake zargin amma jami’an ‘yansanda sun samu nasarar gano maboyar barayin, inda suka ceto wanda aka sace tare da cafke wasu da ake zargi.

Ya ce an samu nasarar kwato bindigar gida guda daya da bindigu na katako guda uku daga hannun wadanda ake zargin.

A halin da ake ciki, daya daga cikin wadanda ake zargin, Sunday Ekwere, ya amsa laifin karbar Naira 850,000 daga kudin fansa da suka karba.sabo

'Yan fashi
Sabo Ahmad
+ postsBio
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    An Gurfanar Da Mutum 3 Bisa Laifin Lakada Wa Wani Duka Har Lahira
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    Dalilin Da Ya Sa Kotu Ta Tasa Keyar Dakta Idris Dutsen Tanshi Zuwa Gidan Yari
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    Uwa Ta Mutu A Kokarin Raba Fada Tsakanin ‘Ya’yanta A Abuja
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    Ta Sayar Da Jariririyarta Domin Ta Biya Bashin Banki

MASU ALAKA

Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Next Post
An Gayyaci CMG Don Ya Zama Babbar Kafar Yada Labarai Kan Gasar Olympics Ta Paris

An Gayyaci CMG Don Ya Zama Babbar Kafar Yada Labarai Kan Gasar Olympics Ta Paris

LABARAI MASU NASABA

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.