ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Kasuwa 2 Sun Mutu, An Ceto 18 Da Igiyar Ruwa Ta Kifar Da Kwale-kwalen Su A Jigawa

by Muhammad
1 year ago
Jigawa

Rundunar Ƴansandan jihar Jigawa a ranar Litinin ta tabbatar da mutuwar mutane biyu, yayin da aka ceto wasu 18 a wani hatsarin kwale-kwale da ya afku a jihar ta Jigawa.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sanda, DSP Lawan Shiisu, ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya fitar a Dutse, ranar Litinin.

  • Kwale-kwale Ya Yi Ajalin Dalibai 2 A Kano
  • Mutane 32 Sun Mutu A Wani Sabon Hatsarin Kwale-kwale A Jihar Taraba

Shiisu ya bayyana cewa rundunar ta samu rahoton lamarin wanda ya faru a ranar Lahadi a kauyen Kwalgai da ke karamar hukumar Auyo da misalin karfe 10 na dare.

ADVERTISEMENT

Ya ce kwale-kwalen ya kife ne a hanyarsa ta zuwa kauyen Hadin da ke karamar hukumar.

Shiisu ya kara da cewa kimanin fasinjoji 20 ne ke cikin jirgin a lokacin da lamarin ya faru.

LABARAI MASU NASABA

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

“A ranar Lahadi da misalin karfe 10:00 na dare, rundunar ‘yansandan ta samu rahoton hatsarin jirgin ruwa daga ofishin ‘yan sanda na Auyo, cewa wasu ‘yan kasuwa daga kauyen Kwalgwai da ke karamar hukumar Auyo sun kai kimanin 20, maza da mata sun hau kwale-kwale ya tintsire da su.

“An ce kwale-kwalen ya kife ne a lokacin da yake tafiya ta rafin Kwalgai zuwa kauyen Hadin da ke karamar hukumar,” in ji Kakakin.

A cewarsa, a kokarin ceto waɗanda lamarin ya rutsa da su, an sanar da masunta da wasu matasan garin don kawo ɗaukin gaggawa, a lokacin da tawagar ‘yan sanda karkashin jagorancin DPO suka garzaya zuwa wurin.

Shisu ya bayyana cewa, tawagar ta samu nasarar ceto fasinjoji 18 da ransu, yayin da wasu biyu kuma dukkansu mata aka neme su aka rasa.

“Daga baya, a yau da misalin karfe 6:00 na safe, an tsinci gawar daya daga cikin fasinjojin mata da suka bata mai suna Habiba Ado ta kauyen Kwalgai.

‘Yansandan sun ce binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa hatsarin ya samo asali ne sakamakon igiyar ruwa mai karfi da kuma yawan lodin da direban ya yi har ya kasa tuka kwalekwalen da kyau.

A cewar Kakakin, ana ci gaba da kokarin ganin an ceto ɗaya matar. Shiisu ya kara da cewa an kai dukkan wadanda aka ceto zuwa asibiti domin duba da lafiyarsu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4
Manyan Labarai

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2
Manyan Labarai

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

November 13, 2025
Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

November 13, 2025
Next Post
‘Yansanda Sun Dakile Harin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Kan Wasu Rukunin Gidaje A Katsina

Rundunar ‘Yansandan Jihar Jigawa Ta Yi Rashin Manyan Jami’anta 3 A Cikin Kwanaki 14

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

November 13, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

November 13, 2025
Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

November 13, 2025
Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

November 13, 2025
Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.