• English
  • Business News
Monday, October 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Kasuwa 2 Sun Mutu, An Ceto 18 Da Igiyar Ruwa Ta Kifar Da Kwale-kwalen Su A Jigawa

by Muhammad
1 year ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Manyan Labarai
0
‘Yan Kasuwa 2 Sun Mutu, An Ceto 18 Da Igiyar Ruwa Ta Kifar Da Kwale-kwalen Su A Jigawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar Ƴansandan jihar Jigawa a ranar Litinin ta tabbatar da mutuwar mutane biyu, yayin da aka ceto wasu 18 a wani hatsarin kwale-kwale da ya afku a jihar ta Jigawa.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sanda, DSP Lawan Shiisu, ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya fitar a Dutse, ranar Litinin.

  • Kwale-kwale Ya Yi Ajalin Dalibai 2 A Kano
  • Mutane 32 Sun Mutu A Wani Sabon Hatsarin Kwale-kwale A Jihar Taraba

Shiisu ya bayyana cewa rundunar ta samu rahoton lamarin wanda ya faru a ranar Lahadi a kauyen Kwalgai da ke karamar hukumar Auyo da misalin karfe 10 na dare.

Ya ce kwale-kwalen ya kife ne a hanyarsa ta zuwa kauyen Hadin da ke karamar hukumar.

Shiisu ya kara da cewa kimanin fasinjoji 20 ne ke cikin jirgin a lokacin da lamarin ya faru.

Labarai Masu Nasaba

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

“A ranar Lahadi da misalin karfe 10:00 na dare, rundunar ‘yansandan ta samu rahoton hatsarin jirgin ruwa daga ofishin ‘yan sanda na Auyo, cewa wasu ‘yan kasuwa daga kauyen Kwalgwai da ke karamar hukumar Auyo sun kai kimanin 20, maza da mata sun hau kwale-kwale ya tintsire da su.

“An ce kwale-kwalen ya kife ne a lokacin da yake tafiya ta rafin Kwalgai zuwa kauyen Hadin da ke karamar hukumar,” in ji Kakakin.

A cewarsa, a kokarin ceto waɗanda lamarin ya rutsa da su, an sanar da masunta da wasu matasan garin don kawo ɗaukin gaggawa, a lokacin da tawagar ‘yan sanda karkashin jagorancin DPO suka garzaya zuwa wurin.

Shisu ya bayyana cewa, tawagar ta samu nasarar ceto fasinjoji 18 da ransu, yayin da wasu biyu kuma dukkansu mata aka neme su aka rasa.

“Daga baya, a yau da misalin karfe 6:00 na safe, an tsinci gawar daya daga cikin fasinjojin mata da suka bata mai suna Habiba Ado ta kauyen Kwalgai.

‘Yansandan sun ce binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa hatsarin ya samo asali ne sakamakon igiyar ruwa mai karfi da kuma yawan lodin da direban ya yi har ya kasa tuka kwalekwalen da kyau.

A cewar Kakakin, ana ci gaba da kokarin ganin an ceto ɗaya matar. Shiisu ya kara da cewa an kai dukkan wadanda aka ceto zuwa asibiti domin duba da lafiyarsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan Kasuwa'Yan SandaCetoHadarin kwale-kwaleJigawaMutuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

’Yan Daba Sun Yi Wa Wata Tsohuwa Mai Shekaru 60 Kisan-Gilla A Bauchi

Next Post

Rundunar ‘Yansandan Jihar Jigawa Ta Yi Rashin Manyan Jami’anta 3 A Cikin Kwanaki 14

Related

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Manyan Labarai

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

16 hours ago
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

1 day ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

1 day ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

2 days ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

2 days ago
NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja
Manyan Labarai

NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

2 days ago
Next Post
‘Yansanda Sun Dakile Harin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Kan Wasu Rukunin Gidaje A Katsina

Rundunar ‘Yansandan Jihar Jigawa Ta Yi Rashin Manyan Jami’anta 3 A Cikin Kwanaki 14

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

October 5, 2025
Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

October 5, 2025
CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

October 5, 2025
Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

October 5, 2025
Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

October 5, 2025
NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

October 5, 2025
Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

October 5, 2025
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

October 5, 2025
Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

October 5, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

October 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.