• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Kasuwa 2 Sun Mutu, An Ceto 18 Da Igiyar Ruwa Ta Kifar Da Kwale-kwalen Su A Jigawa

by Muhammad
12 months ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Manyan Labarai
0
‘Yan Kasuwa 2 Sun Mutu, An Ceto 18 Da Igiyar Ruwa Ta Kifar Da Kwale-kwalen Su A Jigawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar Ƴansandan jihar Jigawa a ranar Litinin ta tabbatar da mutuwar mutane biyu, yayin da aka ceto wasu 18 a wani hatsarin kwale-kwale da ya afku a jihar ta Jigawa.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sanda, DSP Lawan Shiisu, ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya fitar a Dutse, ranar Litinin.

  • Kwale-kwale Ya Yi Ajalin Dalibai 2 A Kano
  • Mutane 32 Sun Mutu A Wani Sabon Hatsarin Kwale-kwale A Jihar Taraba

Shiisu ya bayyana cewa rundunar ta samu rahoton lamarin wanda ya faru a ranar Lahadi a kauyen Kwalgai da ke karamar hukumar Auyo da misalin karfe 10 na dare.

Ya ce kwale-kwalen ya kife ne a hanyarsa ta zuwa kauyen Hadin da ke karamar hukumar.

Shiisu ya kara da cewa kimanin fasinjoji 20 ne ke cikin jirgin a lokacin da lamarin ya faru.

Labarai Masu Nasaba

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

“A ranar Lahadi da misalin karfe 10:00 na dare, rundunar ‘yansandan ta samu rahoton hatsarin jirgin ruwa daga ofishin ‘yan sanda na Auyo, cewa wasu ‘yan kasuwa daga kauyen Kwalgwai da ke karamar hukumar Auyo sun kai kimanin 20, maza da mata sun hau kwale-kwale ya tintsire da su.

“An ce kwale-kwalen ya kife ne a lokacin da yake tafiya ta rafin Kwalgai zuwa kauyen Hadin da ke karamar hukumar,” in ji Kakakin.

A cewarsa, a kokarin ceto waɗanda lamarin ya rutsa da su, an sanar da masunta da wasu matasan garin don kawo ɗaukin gaggawa, a lokacin da tawagar ‘yan sanda karkashin jagorancin DPO suka garzaya zuwa wurin.

Shisu ya bayyana cewa, tawagar ta samu nasarar ceto fasinjoji 18 da ransu, yayin da wasu biyu kuma dukkansu mata aka neme su aka rasa.

“Daga baya, a yau da misalin karfe 6:00 na safe, an tsinci gawar daya daga cikin fasinjojin mata da suka bata mai suna Habiba Ado ta kauyen Kwalgai.

‘Yansandan sun ce binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa hatsarin ya samo asali ne sakamakon igiyar ruwa mai karfi da kuma yawan lodin da direban ya yi har ya kasa tuka kwalekwalen da kyau.

A cewar Kakakin, ana ci gaba da kokarin ganin an ceto ɗaya matar. Shiisu ya kara da cewa an kai dukkan wadanda aka ceto zuwa asibiti domin duba da lafiyarsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan Kasuwa'Yan SandaCetoHadarin kwale-kwaleJigawaMutuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

’Yan Daba Sun Yi Wa Wata Tsohuwa Mai Shekaru 60 Kisan-Gilla A Bauchi

Next Post

Rundunar ‘Yansandan Jihar Jigawa Ta Yi Rashin Manyan Jami’anta 3 A Cikin Kwanaki 14

Related

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano
Manyan Labarai

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

7 hours ago
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

12 hours ago
Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata
Manyan Labarai

Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

16 hours ago
Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama
Manyan Labarai

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

18 hours ago
Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC
Manyan Labarai

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

19 hours ago
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

1 day ago
Next Post
‘Yansanda Sun Dakile Harin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Kan Wasu Rukunin Gidaje A Katsina

Rundunar ‘Yansandan Jihar Jigawa Ta Yi Rashin Manyan Jami’anta 3 A Cikin Kwanaki 14

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.