ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Kasuwa 2 Sun Mutu, An Ceto 18 Da Igiyar Ruwa Ta Kifar Da Kwale-kwalen Su A Jigawa

by Muhammad
2 years ago
Jigawa

Rundunar Ƴansandan jihar Jigawa a ranar Litinin ta tabbatar da mutuwar mutane biyu, yayin da aka ceto wasu 18 a wani hatsarin kwale-kwale da ya afku a jihar ta Jigawa.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sanda, DSP Lawan Shiisu, ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya fitar a Dutse, ranar Litinin.

  • Kwale-kwale Ya Yi Ajalin Dalibai 2 A Kano
  • Mutane 32 Sun Mutu A Wani Sabon Hatsarin Kwale-kwale A Jihar Taraba

Shiisu ya bayyana cewa rundunar ta samu rahoton lamarin wanda ya faru a ranar Lahadi a kauyen Kwalgai da ke karamar hukumar Auyo da misalin karfe 10 na dare.

ADVERTISEMENT

Ya ce kwale-kwalen ya kife ne a hanyarsa ta zuwa kauyen Hadin da ke karamar hukumar.

Shiisu ya kara da cewa kimanin fasinjoji 20 ne ke cikin jirgin a lokacin da lamarin ya faru.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

“A ranar Lahadi da misalin karfe 10:00 na dare, rundunar ‘yansandan ta samu rahoton hatsarin jirgin ruwa daga ofishin ‘yan sanda na Auyo, cewa wasu ‘yan kasuwa daga kauyen Kwalgwai da ke karamar hukumar Auyo sun kai kimanin 20, maza da mata sun hau kwale-kwale ya tintsire da su.

“An ce kwale-kwalen ya kife ne a lokacin da yake tafiya ta rafin Kwalgai zuwa kauyen Hadin da ke karamar hukumar,” in ji Kakakin.

A cewarsa, a kokarin ceto waɗanda lamarin ya rutsa da su, an sanar da masunta da wasu matasan garin don kawo ɗaukin gaggawa, a lokacin da tawagar ‘yan sanda karkashin jagorancin DPO suka garzaya zuwa wurin.

Shisu ya bayyana cewa, tawagar ta samu nasarar ceto fasinjoji 18 da ransu, yayin da wasu biyu kuma dukkansu mata aka neme su aka rasa.

“Daga baya, a yau da misalin karfe 6:00 na safe, an tsinci gawar daya daga cikin fasinjojin mata da suka bata mai suna Habiba Ado ta kauyen Kwalgai.

‘Yansandan sun ce binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa hatsarin ya samo asali ne sakamakon igiyar ruwa mai karfi da kuma yawan lodin da direban ya yi har ya kasa tuka kwalekwalen da kyau.

A cewar Kakakin, ana ci gaba da kokarin ganin an ceto ɗaya matar. Shiisu ya kara da cewa an kai dukkan wadanda aka ceto zuwa asibiti domin duba da lafiyarsu.

Jigawa
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
‘Yansanda Sun Dakile Harin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Kan Wasu Rukunin Gidaje A Katsina

Rundunar ‘Yansandan Jihar Jigawa Ta Yi Rashin Manyan Jami’anta 3 A Cikin Kwanaki 14

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.