• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akwai dai takun saka a babbar jam’iyyar adawa ta PDP, biyo bayan barazanar ficewa daga jam’iyyar da ‘yan majalisar tarayya kusan 60 suka yi kan zargin jam’iyyar APC mai mulki ne ke kulawa da kwamitin gudanarwa na jam’iyyar PDP.

Barazanar ‘yan majalisar dai ya biyo bayan nadin kwamitocin rikon kwarya na jam’iyyar PDP a Ribas da wasu jihohin kasar nan, wanda kwamitin gudanarwa na jam’iyyar karkashin jagorancin Umar Damagum ya yi.

  • Liu Yuxi Ya Halarci Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kan Sin Da Afirka Karo Na Uku
  • Yawan Motocin Da Sin Ta Sayar Ya Kai Miliyan 6.72 A Rubu’in Farkon Bana

A yayin wani taron manema labarai a Abuja, ‘yan majalisan sun bukaci a tsige Damagum daga mukaminsa na rikon kwarya na shugaban jam’iyyar PDP na kasa, inda suka yi gargadin cewa idan ba a yi haka ba, za su fice daga jam’iyyar.

Da suke magana kan zargin, masu magana da yawun gamayyar ‘yan majalisan dokokin na PDP, Hon. Ikenga Imo Ugochinyere, Hon. Aliyu Mustapha (Kaduna), Hon. Awaji-Inombek Abiante (Ribas), Hon. Midala Balami (Borno) da wasu da dama, sun yi watsi da matakin mukaddashin shugaban jam’iyyar PDP na kasa, na neman murkushe magoya bayan PDP tare da fifita ‘yan jam’iyyar APC, musamman a Jihar Ribas.

A cewar ‘yan majalisan, za su taimaka wa mukaddashin shugaban wanda yake rike da mukamin ba bisa ka’ida ba, wajen ruguza jam’iyyar PDP idan har bai janye matakin ba tare da duba jerin sunayen kwamitocin riko na Jihar Ribas da sauran jihohi 16.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

‘Yan majalisan sun kuma yi kira ga Damagum da ya yi murabus daga mukaminsa cikin gaggawa don ba da damar wani daga shiyyar Arewa ta tsakiya ya maye gurbinsa na kulawa da al’amuran jam’iyyar PDP bisa bin tsarin doka na ganin wani daga yankin Arewa ta tsakiya ya gaji tsohon shugaban jam’iyyar na kasa, Sanata Iyorchia Ayu da ya fito daga Jihar Benuwai, wanda aka tsige shi a ranar 28 ga Maris, 2023.

Sun sha alwashin taimaka wa Damagum wajen ruguza PDP idan ya ki cire ‘yan APC daga mambobin kwamitin riko na PDP a Ribas da wasu jihohi 16.

‘Yan majalisan sun dai zargi Damagun da nada ‘ya’yan jam’iyyar APC a cikin kwamitin riko na PDP na kananan hukumomi a Jihar Ribas da wasu jihohi da dama. Sun ce wannan mataki na iya kashe jam’iyyar PDP.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

APC Da PDP, Duk Kanwar Ja Ce -Kwankwaso

Next Post

Sin Na Adawa Da Amurka Da Ta Girke Makamai Masu Linzami A Yankin Asiya-Pasifik

Related

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

7 days ago
PDP
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

1 week ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

1 week ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

2 weeks ago
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

2 weeks ago
arewa
Tambarin Dimokuradiyya

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

2 weeks ago
Next Post
Sin Na Adawa Da Amurka Da Ta Girke Makamai Masu Linzami A Yankin Asiya-Pasifik

Sin Na Adawa Da Amurka Da Ta Girke Makamai Masu Linzami A Yankin Asiya-Pasifik

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

May 9, 2025
Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

May 9, 2025
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta ÆŠage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta ÆŠage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.