• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
PDP

Akwai dai takun saka a babbar jam’iyyar adawa ta PDP, biyo bayan barazanar ficewa daga jam’iyyar da ‘yan majalisar tarayya kusan 60 suka yi kan zargin jam’iyyar APC mai mulki ne ke kulawa da kwamitin gudanarwa na jam’iyyar PDP.

Barazanar ‘yan majalisar dai ya biyo bayan nadin kwamitocin rikon kwarya na jam’iyyar PDP a Ribas da wasu jihohin kasar nan, wanda kwamitin gudanarwa na jam’iyyar karkashin jagorancin Umar Damagum ya yi.

  • Liu Yuxi Ya Halarci Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kan Sin Da Afirka Karo Na Uku
  • Yawan Motocin Da Sin Ta Sayar Ya Kai Miliyan 6.72 A Rubu’in Farkon Bana

A yayin wani taron manema labarai a Abuja, ‘yan majalisan sun bukaci a tsige Damagum daga mukaminsa na rikon kwarya na shugaban jam’iyyar PDP na kasa, inda suka yi gargadin cewa idan ba a yi haka ba, za su fice daga jam’iyyar.

Da suke magana kan zargin, masu magana da yawun gamayyar ‘yan majalisan dokokin na PDP, Hon. Ikenga Imo Ugochinyere, Hon. Aliyu Mustapha (Kaduna), Hon. Awaji-Inombek Abiante (Ribas), Hon. Midala Balami (Borno) da wasu da dama, sun yi watsi da matakin mukaddashin shugaban jam’iyyar PDP na kasa, na neman murkushe magoya bayan PDP tare da fifita ‘yan jam’iyyar APC, musamman a Jihar Ribas.

A cewar ‘yan majalisan, za su taimaka wa mukaddashin shugaban wanda yake rike da mukamin ba bisa ka’ida ba, wajen ruguza jam’iyyar PDP idan har bai janye matakin ba tare da duba jerin sunayen kwamitocin riko na Jihar Ribas da sauran jihohi 16.

LABARAI MASU NASABA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

‘Yan majalisan sun kuma yi kira ga Damagum da ya yi murabus daga mukaminsa cikin gaggawa don ba da damar wani daga shiyyar Arewa ta tsakiya ya maye gurbinsa na kulawa da al’amuran jam’iyyar PDP bisa bin tsarin doka na ganin wani daga yankin Arewa ta tsakiya ya gaji tsohon shugaban jam’iyyar na kasa, Sanata Iyorchia Ayu da ya fito daga Jihar Benuwai, wanda aka tsige shi a ranar 28 ga Maris, 2023.

Sun sha alwashin taimaka wa Damagum wajen ruguza PDP idan ya ki cire ‘yan APC daga mambobin kwamitin riko na PDP a Ribas da wasu jihohi 16.

‘Yan majalisan sun dai zargi Damagun da nada ‘ya’yan jam’iyyar APC a cikin kwamitin riko na PDP na kananan hukumomi a Jihar Ribas da wasu jihohi da dama. Sun ce wannan mataki na iya kashe jam’iyyar PDP.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
Tambarin Dimokuradiyya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
Next Post
Sin Na Adawa Da Amurka Da Ta Girke Makamai Masu Linzami A Yankin Asiya-Pasifik

Sin Na Adawa Da Amurka Da Ta Girke Makamai Masu Linzami A Yankin Asiya-Pasifik

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

November 8, 2025
Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.