• English
  • Business News
Sunday, June 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akwai dai takun saka a babbar jam’iyyar adawa ta PDP, biyo bayan barazanar ficewa daga jam’iyyar da ‘yan majalisar tarayya kusan 60 suka yi kan zargin jam’iyyar APC mai mulki ne ke kulawa da kwamitin gudanarwa na jam’iyyar PDP.

Barazanar ‘yan majalisar dai ya biyo bayan nadin kwamitocin rikon kwarya na jam’iyyar PDP a Ribas da wasu jihohin kasar nan, wanda kwamitin gudanarwa na jam’iyyar karkashin jagorancin Umar Damagum ya yi.

  • Liu Yuxi Ya Halarci Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kan Sin Da Afirka Karo Na Uku
  • Yawan Motocin Da Sin Ta Sayar Ya Kai Miliyan 6.72 A Rubu’in Farkon Bana

A yayin wani taron manema labarai a Abuja, ‘yan majalisan sun bukaci a tsige Damagum daga mukaminsa na rikon kwarya na shugaban jam’iyyar PDP na kasa, inda suka yi gargadin cewa idan ba a yi haka ba, za su fice daga jam’iyyar.

Da suke magana kan zargin, masu magana da yawun gamayyar ‘yan majalisan dokokin na PDP, Hon. Ikenga Imo Ugochinyere, Hon. Aliyu Mustapha (Kaduna), Hon. Awaji-Inombek Abiante (Ribas), Hon. Midala Balami (Borno) da wasu da dama, sun yi watsi da matakin mukaddashin shugaban jam’iyyar PDP na kasa, na neman murkushe magoya bayan PDP tare da fifita ‘yan jam’iyyar APC, musamman a Jihar Ribas.

A cewar ‘yan majalisan, za su taimaka wa mukaddashin shugaban wanda yake rike da mukamin ba bisa ka’ida ba, wajen ruguza jam’iyyar PDP idan har bai janye matakin ba tare da duba jerin sunayen kwamitocin riko na Jihar Ribas da sauran jihohi 16.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

‘Yan majalisan sun kuma yi kira ga Damagum da ya yi murabus daga mukaminsa cikin gaggawa don ba da damar wani daga shiyyar Arewa ta tsakiya ya maye gurbinsa na kulawa da al’amuran jam’iyyar PDP bisa bin tsarin doka na ganin wani daga yankin Arewa ta tsakiya ya gaji tsohon shugaban jam’iyyar na kasa, Sanata Iyorchia Ayu da ya fito daga Jihar Benuwai, wanda aka tsige shi a ranar 28 ga Maris, 2023.

Sun sha alwashin taimaka wa Damagum wajen ruguza PDP idan ya ki cire ‘yan APC daga mambobin kwamitin riko na PDP a Ribas da wasu jihohi 16.

‘Yan majalisan sun dai zargi Damagun da nada ‘ya’yan jam’iyyar APC a cikin kwamitin riko na PDP na kananan hukumomi a Jihar Ribas da wasu jihohi da dama. Sun ce wannan mataki na iya kashe jam’iyyar PDP.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

APC Da PDP, Duk Kanwar Ja Ce -Kwankwaso

Next Post

Sin Na Adawa Da Amurka Da Ta Girke Makamai Masu Linzami A Yankin Asiya-Pasifik

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

1 week ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

1 week ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

2 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

3 weeks ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

4 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
Sin Na Adawa Da Amurka Da Ta Girke Makamai Masu Linzami A Yankin Asiya-Pasifik

Sin Na Adawa Da Amurka Da Ta Girke Makamai Masu Linzami A Yankin Asiya-Pasifik

LABARAI MASU NASABA

Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

June 22, 2025
Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?

Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?

June 22, 2025
Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona

Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona

June 22, 2025
Tinubu Ya Yi Allah-Wadai Da Harin Bam A Borno, Ya Yi Alhinin Fashewar Wani A Kano

Tinubu Ya Yi Allah-Wadai Da Harin Bam A Borno, Ya Yi Alhinin Fashewar Wani A Kano

June 22, 2025
Gwamnatin Hong Kong Ta Gudanar Da Bikin Cika Shekaru Biyar Da Kafuwar Dokar Tsaron Kasa Ta Yankin

Gwamnatin Hong Kong Ta Gudanar Da Bikin Cika Shekaru Biyar Da Kafuwar Dokar Tsaron Kasa Ta Yankin

June 22, 2025
Barayin Wayar Lantarki Sun Addabi A’lummar Jihar Kebbi

Barayin Wayar Lantarki Sun Addabi A’lummar Jihar Kebbi

June 22, 2025
Sin Ta Yi Matukar Allah Wadai Da Hare-Haren Da Amurka Ta Kaiwa Iran

Sin Ta Yi Matukar Allah Wadai Da Hare-Haren Da Amurka Ta Kaiwa Iran

June 22, 2025
Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)

Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)

June 22, 2025
Bernado Silba Ya Zama Sabon Kyaftin Din Manchester City 

Bernado Silba Ya Zama Sabon Kyaftin Din Manchester City 

June 22, 2025
Harin Amurka A Wurare 3 Na Nukiliyar Iran: Babu Wani Lahani A Harin Bama-baman – Iran

Harin Amurka A Wurare 3 Na Nukiliyar Iran: Babu Wani Lahani A Harin Bama-baman – Iran

June 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.