• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Majalisu Tara Da Ke Zawarcin Kujerar Gbajabiamila

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
‘Yan Majalisu Tara Da Ke Zawarcin Kujerar Gbajabiamila
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Adadin ‘yan majalisar wakilai da ke sa ido a kan kujerar shugaban majalisar wakilai ta 10 a yanzu ya kai tara.

Hakan dai na faruwa ne duk da cewa an sake zaben shugaban majalisar mai ci Femi Gbajabiamila a karo na shida kuma zai kasance a majalisar.

  • Ba A Taba Zabe A Nijeriya Mai Karancin Tashe-tashen Hankula Kamar Na 2023 Ba – Gwamnatin Tarayya

A watan Yunin shekarar 2019 ne dai aka kaddamar da majalisar wakilai mai ci a yanzu, kuma ana sa ran za a kaddamar da majalisa ta 10 a irin wannan wata na shekaran nan.

A ranar Talata ne, Abdulraheem Olawuyi dan majalisa mai wakiltar mazabar Ekiti/Isin/Irepodun/Oke-Ero a Jihar Kwara ya shirya bayyana sha’awar zama shugaban majalisar.

A cewar wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, ana sa ran Olawuyi zai bayyana aniyarsa ta neman kujerar ranar Talata a Abuja a hukumance.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

Olawuyi wanda shi ne shugaban kwamitin majalisar kan ba da agajin gaggawa da shirye-shiryen jinkai, ya ce ya yi tuntubar juna sosai kan aniyarsa ta tsayawa takarar shugabancin majalisa kuma ya ji dadin yadda ya samu goyon baya.

A cikin sanarwar mai taken, ‘AbdulRaheem ya shiga takarar shugaban majalisar, zai bayyana ranar 4 ga Afrilu a hukumance’, ya ce ya yi imanin cewa ya mallaki kwarewar da ake bukata don samun shugaban mai inganta idan abokan aikinsa suka zabe shi.
Ya ce tsofaffi da sabbin mambobin majalisar za su halarci sanarwar a hukumance.

“Ina mai tabbatar muku da cewa idan aka zabe ni, zan yi kokarin inganta manufofin da za su amfanar da daukacin ‘yan Nijeriya daga sassa daban-daban, kuma za mu yi aiki tare da dukkan bangarorin domin hada kan kasa. Ina matukar fatan haduwa da ’yan’uwana ’yan majalisa tare da bayyana musu ra’ayina, da kuma sauraron ra’ayoyinsu kan yadda za a inganta rayuwar jama’a idan aka zabe ni a matsayin shugaban majalisar wakilai,” in ji Olawuyi.

Dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Mallammadori/Kaugama a Jihar Jigawa kuma mataimakin shugaban kwamitin tsaro na majalisar, Abubakar Yalleman, ya bayyana aniyarsa ta zama shugaban majalisan wakilai a makon jiya.

Mataimakin shugaban majalisar, Ahmed Wase da shugaban masu rinjaye, Alhassan Ado-Doguwa da shugaban kwamitin majalisar kan harkokin sojojin ruwa, Yusuf Gagdi da shugaban kwamitin kasafin kudi na majalisar, Aliyu Betara da shugaban kwamitin majalisar kan cibiyoyin bincike na kimiyya, Olaide Akinremi da shugaban kwamitin majalisar kan harkokin yada labarai da hulda da jama’a, Benjamin Kalu da kuma shugaban kwamitin sufuri na kasa, Tajudeen Abbas, dukkansu suna cikin wadanda suka nuna sha’awarsu na neman shugabancin majalisar wakilai.

Wase ya fito ne daga Filato a shiyyar Arewa ta tsakiya, Ado-Doguwa ya fito daga Kano a Arewa maso Yamma, Gagdi yana wakiltar Filato a Arewa ta Tsakiya, Betara ya fito daga Borno a Arewa maso Gabas, Akinremi yana wakiltar Oyo a Kudu maso Yamma, Kalu daga Abiya a Kudu maso Gabas, Yalleman daga Jigawa a Arewa maso Yamma, sannan Abbas daga Kaduna a Arewa maso Yamma.
Sai dai kuma kan ‘yan majalisar ya rabu dangane da yankin da za a bai wa shugabancin majalisan a wannan karo.

Tuni dai Wase ya fara ziyartar manyan masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC da ke fadin kasar nan, a wani bangare na kokarin nuna goyon baya ga burinsa.

Hakazalika, a bangaren majalisar dattawa kuwa, wasu mambobi biyu sun fito fili sun bayyana aniyarsu ta shugabancin majalisar. ‘Yan majalisan dai sun hada da shugaban masu rinjaye, Sanata Orji Kalu da kuma shugaban kwamitin kasafin kudi na majalisar dattawa, Jibrin Barau.

Tsohon shugaban marasa rinjaye, Sanata Godswill Akpabio da shugaban kwamitin ayyuka na majalisar dattawa, Sani Musa har yanzu ba su bayyana tsayawa takarar shugabancin majalisar ba a hukumance, amma masu goyon bayansu a ciki da wajen zauren majalisar sun yi ta magana a kansu.
Shugaban majalisar dattawa mai ci, Ahmad Lawan zai koma zauren majalisa a majalisa mai zuwa.

Shugabannin jam’iyya mai mulki na kasa sun gana da zababbun ‘yan majalisar tarayya a Abuja a ranar 6 ga Maris, 2023, inda aka tattaunawa a kan shugabancin karba-karba na shiyya-shiyya har zuwa bayan zaben gwamnoni da na majalisun jihohi da aka gudanar a ranar 18 ga Maris.

APC ba ta gana da zababbun ‘yan majalisar ba makonni biyu bayan kammala zaben.
A halin da ake ciki kuma, dan majalisar wakilai daga Jihar Kano, Shamsudeen Dambazau, ya bukaci jam’iyyar APC ta mika shugaban majalisar dattawa a yankin Arewa maso Yamma, yayin da ya kafe Jibrin ya hau kujerar.

Dambazau wanda ke wakiltar mazabar Takai/Sumaila ta Kano, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a mai taken ‘Majalisar Tarayya ta 10: Me ya sa APC ba za ta bayar da shugabancin majalisan dattawa ga yankin Arewa maso Yamma da kuma dalilin da zai sa Barau Jibrin zai iya zama shugaban majalisar dattawa na gaba, ya lissafo nasarorin da jam’iyyar ta samu a wannan yanki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Buhari Ya Gaza Gudanar Da Sahihin Zabe A 2023 – Kwankwaso

Next Post

An Samu Tsohuwar Hedimasta Da Laifin Yi Wa Dalibai Fyade

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

1 week ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

1 week ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

1 week ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

2 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

2 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

2 weeks ago
Next Post
'Yan majalisu

An Samu Tsohuwar Hedimasta Da Laifin Yi Wa Dalibai Fyade

LABARAI MASU NASABA

Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.