• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Miliyan 33 Na Iya Fuskantar Matsalar Rashin Abinci A 2025 —Rahoto

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
11 months ago
Abinci

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

Indabawa

Rahoton Cadre Harmonisé na Oktoba ya yi hasashen cewa akalla mutum miliyan 33.1 a cikin jihohi 26 da FCT za su fuskanci matsalar rashin abinci da abinci mai gina jiki tsakanin Yuni da Agusta 2025.
Hukumar Kula Da Abinci Da Noma ta Majalisar Dinkin Duniya, da Hukumar Samar Da Abinci ta Duniya, da Ma’aikatar Noma da Samar Da Abinci Ta Tarayya, da sauran abokan hulda ne suka gudanar da binciken.
Sauran jihohin da abin ya shafa sun hada da Cross Riber, Enugu, Edo, Abia, Kogi, Nasarawa, Kwara, Ogun, Lagas, Ribas, da FCT.
Rahoton ya nuna cewa wannan adadi ya hada da ‘yan gudun hijira 514,474 a Borno, Sakkkwato, da Zamfara.
Ya bayyana cewa kusan mutum miliyan 25 a fadin jihohi 26 da FCT a halin yanzu suna fuskantar matsalar abinci.
“Muna fuskantar kalubalen da ba a taba ganin irinsa ba wanda ya shafi rayuwa da abinci da mai gina jiki a duniya yanku da kasa baki daya.”
Koffy ya ce Nijeriya na fama da tashe-tashen hankula da suka hada da tattalin arziki da suka shafi farashin amfanin gona da noma.
Kayayyaki, abubuwan da suka shafi yanayi kamar ambaliyar ruwa da fari, da rashin tsaro.
Ya bayyana cewa, makasudin taron na CH shi ne nazartar bayanan samar da abinci da kuma abubuwan da ke taimakawa wajen gano yawan jama’a da wuraren da ke fuskantar barazanar karancin abinci mai gina jiki a kasar.
A cewarsa, wadannan tarurrukan kuma suna da nufin ba da shawarar matakan da suka dace don hana ko rage matsalolin abinci da ke faruwa.
Ya ce, “Bincike na CH shi ne mafi aminci, kuma kayan aiki na farko da aka yarda da su don shirye-shiryen jin kai su ne, samar da abinci, da mayar da martani ga rayuwa, da kuma ba da fifikon shirye-shiryen ci gaba.”
Babban Sakataren Ma’aikatar Noma da Samar da Abinci ta Tarayya Temitope Fashedemi, ya yi alkawarin gwamnatin kasar na yin amfani da sakamakon rahoton don jagorantar shirye-shiryen samar da abinci da abinci mai gina jiki a fadin jihohi.
Babban jami’in CH mai kula da shirin samar da abinci na kasa Balama Dauda, ya bayyana manyan abubuwan da ke haddasa matsalar karancin abinci da tsadar kayan masarufi, da ambaliya, da rashin tsaro.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya
Rahotonni

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

October 4, 2025
Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin
Rahotonni

Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin

October 3, 2025
Next Post
Rundunar Soji Ta Ƙaryata Jita-jitar Mutuwar COAS Lagbaja.

Ana Ci Gaba Da Jimamin Rasuwar Shugaban Sojin Nijeriya Lagbaja

LABARAI MASU NASABA

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.