ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Miliyan 95 Za Su Yi Zabe A 2023 —INEC

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
INEC

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana cewa ‘yan Nijeriya miliyan 95 ne za su yi zabe a 2023.

Ta kara da cewa ba dukkan wadanda suka yi rajisitan katin zaben da aka kammala a wannan makon za su samu damar jefa kuri’a.

  • NIS Ta Sauya Wuraren Aiki Ga Manyan Jami’ai 69
  • Gwamnatin Gombe Ta Kafa Kwamitin Sayarwa Da Raba Takin Zamani Don Saukaka Wa Manoma 

Kwamishinan yada labarai na hukumar INEC, Mista Festus Okoye shi ya bayyana hakan a ranar Litinin yayin gudanar da wani shiri a gidan talabijin na Arise Tb.

ADVERTISEMENT

Okoye ya bayyana adadin yawan wadanda za su jefa kuri’a a zaben 2023, wanda adadinsu ya kai miliyan 95.

A cewarsa, akwai yuwuwar hukumar za ta cire da yawan wadanda suka yi rajistar daga kididdigar hukumar tare da hana su katin zabe saboda sun yi rajista fiye da guda daya.

LABARAI MASU NASABA

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

Okoye ya tunatar da cewa na farko da na biyu na aikin yin rajistan, an cire fiye da kashi 46 na wadanda suka yi rajista daga kididdigar hukumar sakamakon yin rajistan fiye da guda daya.

Ya ce, “Abun takaice ne a ce an kammala yin katin zabe a yanzu, amma saboda za mu hada dukkan kididdigan wadanda suka amshi katin zabe da muka kammala a kwanan nan tare da amfani da na’urarmu mu cire wadanda suka yi rajista fiye da guda daya.

“Kamar yadda muka sanar, lokacin da muka kammala goje adadin wadanda suka ka yi rajista fiye da guda daya na farko da na biyun aikin rajistar, mun cire sama da kashi 46 wadanda suka yi rajista fiye da guda daya.

Domin haka, za mu yi haka a aikinmu na uku da na hudu domin goje wadanda suka yi rajista fiye da daya.

“Bayan haka, za mu yi hakan a dukkan bayananimu, saboda sashin na 19 (1) na dokar zabe na 2022, ta tilasta wa hukumar zabe ta bayyana wadanda suka yi rajistar zabe a dukkan wuraren yin katin zabe da ke kananan hukumomin Nijeriya guda 8,809.

“Muna tsammanin za a samu wadanda suka yi rajistar zabe guda miliyan 95, inda za mu lika hotunan sama da miliyan 20 a shafi guda dubu biyar a wadannan wuraren rajista, daga baya sai mu lika sauran da suka rage.”

Kwamishinan INEC ya kara da cewa ba dole ba ne a sake kara wa’adin yin rajistan zabe, saboda idan har aka kara, to zai shafi sauran wasu ayyukan na shirye-shiryen zaben 2023.

Ya ce, “Mun bayar da isasshen lokaci ga wadanda suka cancanci yin rajistan zabe, wanda muka bayar da tazarar yin rajistar har na tsawon watanni 13.

“Lokacin da muka kara wa’adin wata daya na yin rajistar zabe, sai da muka kara yin hayan ma’aikata a dukkan wuraren yin katin zabe, sannan mun kara wasu na’urori a dukkan cibiyoyin yin rajista da suka gudana.

Haka kuma mun kara lokacin yin katin zaben tun daga karfe tara har zuwa karfe biyar na yamma, ciki har da ranakun Asabar da Lahadi.

Amma abun takaicin shi ne, mun kammala wannan aiki a ce sai mun kara wani wa’adi, aikinmu na zabe muna tafiyartar da shi ne kamar yadda doka ta tanada. Idan muka kara wani wa’adin yin rajista, to zai shafi jaddawalin ayyukan zaben 2023.”

Kwamishinan ya cewa sun bai wa jama’a duk irin lokacin da suke bukata don mallakar katin zabe. A kan haka ya ce ba za su sake tsawaita lokacin yankar rajistar ba, lura da yadda lokaci ke kara kure musu.

INEC ta ce tana so ta mayar da hankali ne ga sauran ayyukan da ke kan jadawalin zaben na 2023, kuma dole sai ta rufe yankar katin ne za ta iya samun ci gaba.

A ranar 28 ga watan Yuni ne, hukumar zaben ta sanar da tsawaita lokacin yin rajistar zuwa ranar 31 ga watan Yulin 2022, bayan bukatar hakan daga bangarori daban-daban na kasar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas
Labarai

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

November 17, 2025
NBS
Labarai

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

November 17, 2025
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

November 17, 2025
Next Post
Matsalolin Da Nijeriya Ke Fuskanta Yanzu Ya Zarce Na 2015 Kafin Zuwan Buhari – Sanusi Lamido

Matsalolin Da Nijeriya Ke Fuskanta Yanzu Ya Zarce Na 2015 Kafin Zuwan Buhari - Sanusi Lamido

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

November 17, 2025
Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

November 17, 2025
An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

November 17, 2025
NBS

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

November 17, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

November 17, 2025
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

November 17, 2025
Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

November 17, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

November 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.