• Leadership Hausa
Tuesday, March 21, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Miliyan 95 Za Su Yi Zabe A 2023 —INEC

by Yusuf Shuaibu
8 months ago
in Labarai
0
‘Yan Nijeriya Miliyan 95 Za Su Yi Zabe A 2023 —INEC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana cewa ‘yan Nijeriya miliyan 95 ne za su yi zabe a 2023.

Ta kara da cewa ba dukkan wadanda suka yi rajisitan katin zaben da aka kammala a wannan makon za su samu damar jefa kuri’a.

  • NIS Ta Sauya Wuraren Aiki Ga Manyan Jami’ai 69
  • Gwamnatin Gombe Ta Kafa Kwamitin Sayarwa Da Raba Takin Zamani Don Saukaka Wa Manoma 

Kwamishinan yada labarai na hukumar INEC, Mista Festus Okoye shi ya bayyana hakan a ranar Litinin yayin gudanar da wani shiri a gidan talabijin na Arise Tb.

Okoye ya bayyana adadin yawan wadanda za su jefa kuri’a a zaben 2023, wanda adadinsu ya kai miliyan 95.

A cewarsa, akwai yuwuwar hukumar za ta cire da yawan wadanda suka yi rajistar daga kididdigar hukumar tare da hana su katin zabe saboda sun yi rajista fiye da guda daya.

Labarai Masu Nasaba

Ramadan: Shehu Isma’ila Mai Diwani Ya Buɗe Tafsirin Alƙur’ani A Kaduna

An Sace Baturen Zabe Akan Hanyarsa Ta Zuwa Cibiyar Tattara Sakamakon Zabe A Zamfara

Okoye ya tunatar da cewa na farko da na biyu na aikin yin rajistan, an cire fiye da kashi 46 na wadanda suka yi rajista daga kididdigar hukumar sakamakon yin rajistan fiye da guda daya.

Ya ce, “Abun takaice ne a ce an kammala yin katin zabe a yanzu, amma saboda za mu hada dukkan kididdigan wadanda suka amshi katin zabe da muka kammala a kwanan nan tare da amfani da na’urarmu mu cire wadanda suka yi rajista fiye da guda daya.

“Kamar yadda muka sanar, lokacin da muka kammala goje adadin wadanda suka ka yi rajista fiye da guda daya na farko da na biyun aikin rajistar, mun cire sama da kashi 46 wadanda suka yi rajista fiye da guda daya.

Domin haka, za mu yi haka a aikinmu na uku da na hudu domin goje wadanda suka yi rajista fiye da daya.

“Bayan haka, za mu yi hakan a dukkan bayananimu, saboda sashin na 19 (1) na dokar zabe na 2022, ta tilasta wa hukumar zabe ta bayyana wadanda suka yi rajistar zabe a dukkan wuraren yin katin zabe da ke kananan hukumomin Nijeriya guda 8,809.

“Muna tsammanin za a samu wadanda suka yi rajistar zabe guda miliyan 95, inda za mu lika hotunan sama da miliyan 20 a shafi guda dubu biyar a wadannan wuraren rajista, daga baya sai mu lika sauran da suka rage.”

Kwamishinan INEC ya kara da cewa ba dole ba ne a sake kara wa’adin yin rajistan zabe, saboda idan har aka kara, to zai shafi sauran wasu ayyukan na shirye-shiryen zaben 2023.

Ya ce, “Mun bayar da isasshen lokaci ga wadanda suka cancanci yin rajistan zabe, wanda muka bayar da tazarar yin rajistar har na tsawon watanni 13.

“Lokacin da muka kara wa’adin wata daya na yin rajistar zabe, sai da muka kara yin hayan ma’aikata a dukkan wuraren yin katin zabe, sannan mun kara wasu na’urori a dukkan cibiyoyin yin rajista da suka gudana.

Haka kuma mun kara lokacin yin katin zaben tun daga karfe tara har zuwa karfe biyar na yamma, ciki har da ranakun Asabar da Lahadi.

Amma abun takaicin shi ne, mun kammala wannan aiki a ce sai mun kara wani wa’adi, aikinmu na zabe muna tafiyartar da shi ne kamar yadda doka ta tanada. Idan muka kara wani wa’adin yin rajista, to zai shafi jaddawalin ayyukan zaben 2023.”

Kwamishinan ya cewa sun bai wa jama’a duk irin lokacin da suke bukata don mallakar katin zabe. A kan haka ya ce ba za su sake tsawaita lokacin yankar rajistar ba, lura da yadda lokaci ke kara kure musu.

INEC ta ce tana so ta mayar da hankali ne ga sauran ayyukan da ke kan jadawalin zaben na 2023, kuma dole sai ta rufe yankar katin ne za ta iya samun ci gaba.

A ranar 28 ga watan Yuni ne, hukumar zaben ta sanar da tsawaita lokacin yin rajistar zuwa ranar 31 ga watan Yulin 2022, bayan bukatar hakan daga bangarori daban-daban na kasar.

Tags: 2023Farfesa MahmoudINECKatin ZabeKuri'aZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dakarun PLA Sun Harba Makamai Masu Rai Yayin Matakan Da Suka Kaddamar A Kusa Da Tsibirin Taiwan

Next Post

Matsalolin Da Nijeriya Ke Fuskanta Yanzu Ya Zarce Na 2015 Kafin Zuwan Buhari – Sanusi Lamido

Related

Ramadan: Shehu Isma’ila Mai Diwani Ya Buɗe Tafsirin Alƙur’ani A Kaduna
Labarai

Ramadan: Shehu Isma’ila Mai Diwani Ya Buɗe Tafsirin Alƙur’ani A Kaduna

11 hours ago
Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo
Labarai

An Sace Baturen Zabe Akan Hanyarsa Ta Zuwa Cibiyar Tattara Sakamakon Zabe A Zamfara

12 hours ago
Gwamna Zulum Ya Sake Lashe Zaben Gwamna A Jihar Borno
Labarai

Gwamna Zulum Ya Sake Lashe Zaben Gwamna A Jihar Borno

13 hours ago
An Kashe ‘Yansanda 2, Da Dama Sun Samu Raunuka A Wata Arangama Da Sojoji A Taraba
Labarai

An Kashe ‘Yansanda 2, Da Dama Sun Samu Raunuka A Wata Arangama Da Sojoji A Taraba

14 hours ago
Ina Kira Ga INEC Ta Gaggauta Sake Sakamakon Zaben Gwamna – Atiku
Labarai

Ina Kira Ga INEC Ta Gaggauta Sake Sakamakon Zaben Gwamna – Atiku

15 hours ago
Da Dumi-dumi: Dan Takarar Gwamnan APC Bago, Ya Lashe Zaben Jihar Neja 
Labarai

Da Dumi-dumi: Dan Takarar Gwamnan APC Bago, Ya Lashe Zaben Jihar Neja 

15 hours ago
Next Post
Matsalolin Da Nijeriya Ke Fuskanta Yanzu Ya Zarce Na 2015 Kafin Zuwan Buhari – Sanusi Lamido

Matsalolin Da Nijeriya Ke Fuskanta Yanzu Ya Zarce Na 2015 Kafin Zuwan Buhari - Sanusi Lamido

LABARAI MASU NASABA

Jihar Zamfara: Dauda Lawal Dare Na Jam’iyyar PDP Ya Kayar Da Gwamna Matawalle Na APC

Jihar Zamfara: Dauda Lawal Dare Na Jam’iyyar PDP Ya Kayar Da Gwamna Matawalle Na APC

March 21, 2023
An Kaddamar Da Shirin Bidiyon “Bayanin Magabata Da Xi Jinping Ke So” Na 2 Da Harshen Rashanci 

An Kaddamar Da Shirin Bidiyon “Bayanin Magabata Da Xi Jinping Ke So” Na 2 Da Harshen Rashanci 

March 20, 2023
Shugaban Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Rasha Vladimir Putin

Shugaban Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Rasha Vladimir Putin

March 20, 2023
Ramadan: Shehu Isma’ila Mai Diwani Ya Buɗe Tafsirin Alƙur’ani A Kaduna

Ramadan: Shehu Isma’ila Mai Diwani Ya Buɗe Tafsirin Alƙur’ani A Kaduna

March 20, 2023
Firaministan Kasar Djibouti Ya Mikawa Tawagar Jiyya Ta Kasar Sin Lambar Yabo

Firaministan Kasar Djibouti Ya Mikawa Tawagar Jiyya Ta Kasar Sin Lambar Yabo

March 20, 2023
Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo

An Sace Baturen Zabe Akan Hanyarsa Ta Zuwa Cibiyar Tattara Sakamakon Zabe A Zamfara

March 20, 2023
Dangantakar Sin Da Rasha Ta Bayyana “Hanyar Da Ta Dace Ta Cudanya Tsakanin Kasa Da Kasa”

Dangantakar Sin Da Rasha Ta Bayyana “Hanyar Da Ta Dace Ta Cudanya Tsakanin Kasa Da Kasa”

March 20, 2023
Gwamna Zulum Ya Sake Lashe Zaben Gwamna A Jihar Borno

Gwamna Zulum Ya Sake Lashe Zaben Gwamna A Jihar Borno

March 20, 2023
An Kashe ‘Yansanda 2, Da Dama Sun Samu Raunuka A Wata Arangama Da Sojoji A Taraba

An Kashe ‘Yansanda 2, Da Dama Sun Samu Raunuka A Wata Arangama Da Sojoji A Taraba

March 20, 2023
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Da Sauran Kasashen Yammacin Duniya Da Su Gaggauta Dage Takunkumin Kan Bangare Daya

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Da Sauran Kasashen Yammacin Duniya Da Su Gaggauta Dage Takunkumin Kan Bangare Daya

March 20, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.