ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Miliyan 95 Za Su Yi Zabe A 2023 —INEC

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
INEC

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana cewa ‘yan Nijeriya miliyan 95 ne za su yi zabe a 2023.

Ta kara da cewa ba dukkan wadanda suka yi rajisitan katin zaben da aka kammala a wannan makon za su samu damar jefa kuri’a.

  • NIS Ta Sauya Wuraren Aiki Ga Manyan Jami’ai 69
  • Gwamnatin Gombe Ta Kafa Kwamitin Sayarwa Da Raba Takin Zamani Don Saukaka Wa Manoma 

Kwamishinan yada labarai na hukumar INEC, Mista Festus Okoye shi ya bayyana hakan a ranar Litinin yayin gudanar da wani shiri a gidan talabijin na Arise Tb.

ADVERTISEMENT

Okoye ya bayyana adadin yawan wadanda za su jefa kuri’a a zaben 2023, wanda adadinsu ya kai miliyan 95.

A cewarsa, akwai yuwuwar hukumar za ta cire da yawan wadanda suka yi rajistar daga kididdigar hukumar tare da hana su katin zabe saboda sun yi rajista fiye da guda daya.

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

Okoye ya tunatar da cewa na farko da na biyu na aikin yin rajistan, an cire fiye da kashi 46 na wadanda suka yi rajista daga kididdigar hukumar sakamakon yin rajistan fiye da guda daya.

Ya ce, “Abun takaice ne a ce an kammala yin katin zabe a yanzu, amma saboda za mu hada dukkan kididdigan wadanda suka amshi katin zabe da muka kammala a kwanan nan tare da amfani da na’urarmu mu cire wadanda suka yi rajista fiye da guda daya.

“Kamar yadda muka sanar, lokacin da muka kammala goje adadin wadanda suka ka yi rajista fiye da guda daya na farko da na biyun aikin rajistar, mun cire sama da kashi 46 wadanda suka yi rajista fiye da guda daya.

Domin haka, za mu yi haka a aikinmu na uku da na hudu domin goje wadanda suka yi rajista fiye da daya.

“Bayan haka, za mu yi hakan a dukkan bayananimu, saboda sashin na 19 (1) na dokar zabe na 2022, ta tilasta wa hukumar zabe ta bayyana wadanda suka yi rajistar zabe a dukkan wuraren yin katin zabe da ke kananan hukumomin Nijeriya guda 8,809.

“Muna tsammanin za a samu wadanda suka yi rajistar zabe guda miliyan 95, inda za mu lika hotunan sama da miliyan 20 a shafi guda dubu biyar a wadannan wuraren rajista, daga baya sai mu lika sauran da suka rage.”

Kwamishinan INEC ya kara da cewa ba dole ba ne a sake kara wa’adin yin rajistan zabe, saboda idan har aka kara, to zai shafi sauran wasu ayyukan na shirye-shiryen zaben 2023.

Ya ce, “Mun bayar da isasshen lokaci ga wadanda suka cancanci yin rajistan zabe, wanda muka bayar da tazarar yin rajistar har na tsawon watanni 13.

“Lokacin da muka kara wa’adin wata daya na yin rajistar zabe, sai da muka kara yin hayan ma’aikata a dukkan wuraren yin katin zabe, sannan mun kara wasu na’urori a dukkan cibiyoyin yin rajista da suka gudana.

Haka kuma mun kara lokacin yin katin zaben tun daga karfe tara har zuwa karfe biyar na yamma, ciki har da ranakun Asabar da Lahadi.

Amma abun takaicin shi ne, mun kammala wannan aiki a ce sai mun kara wani wa’adi, aikinmu na zabe muna tafiyartar da shi ne kamar yadda doka ta tanada. Idan muka kara wani wa’adin yin rajista, to zai shafi jaddawalin ayyukan zaben 2023.”

Kwamishinan ya cewa sun bai wa jama’a duk irin lokacin da suke bukata don mallakar katin zabe. A kan haka ya ce ba za su sake tsawaita lokacin yankar rajistar ba, lura da yadda lokaci ke kara kure musu.

INEC ta ce tana so ta mayar da hankali ne ga sauran ayyukan da ke kan jadawalin zaben na 2023, kuma dole sai ta rufe yankar katin ne za ta iya samun ci gaba.

A ranar 28 ga watan Yuni ne, hukumar zaben ta sanar da tsawaita lokacin yin rajistar zuwa ranar 31 ga watan Yulin 2022, bayan bukatar hakan daga bangarori daban-daban na kasar.

INEC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Next Post
Matsalolin Da Nijeriya Ke Fuskanta Yanzu Ya Zarce Na 2015 Kafin Zuwan Buhari – Sanusi Lamido

Matsalolin Da Nijeriya Ke Fuskanta Yanzu Ya Zarce Na 2015 Kafin Zuwan Buhari - Sanusi Lamido

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.