ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Na Da Riko Da Addini, Amma Hakan Bai Hana Su Sata Da Zamba Ba – Buhari

by Sadiq
4 years ago
Buhari

Shugaba Buhari ya ce za a iya kawar da mafi yawan kalubalen da ke addabar al’ummar kasar nan idan har da gaske ‘yan Nijeriya suka yi amfani da koyarwar addininsu.

A sakonsa na sallah ga ‘yan Nijeriya, shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya ce ya kamata ‘yan Nijeriya su yi amfani da addini a matsayin abin da zai karfafa soyayyar bil Adama a tsakaninsu.

  • NAHCON Ta Nemi Afuwa Kan Gaza Kwashe Maniyyata 1,551 Zuwa Aikin Hajji
  • ‘Yan Nijeriya Sun Yi Alhinin Rasuwar Babban Sakataren OPEC Sanusi Barkindo

A cewar wata sanarwa da Garba Shehu, mai magana da yawun shugaban kasa Buhari ya fitar, ya ce da ‘yan Nijeriya za su yi amfani da koyarwar addininsu, da an magance mafi yawan abubuwan da suka addabi al’umma.

ADVERTISEMENT

“Mutane suna yin addini ba tare da tsoron Allah ba; suna sa rayuwa ta yi wa wasu wahala; kudi ya zama Allahnsu; Shugabanni sun watsi da rantsuwar da suka yi ta hanyar karbar kudaden da ake bukata don jin dadin jama’a suna karkatar da su zuwa aljihunsu a boye.

“Cutar da jama’a da ‘yan kasuwa ke yi da sace-sacen jama’a da ma’aikatan gwamnati da sauran masu rike da amanar jama’a ke yi, ya nuna yadda aka yi watsi da koyarwar addininmu.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

“Bai kamata a yi amfani da addini kawai a matsayin alama ta ainihi ba, sai dai a matsayin kyautata ruhi don kyautatawa kasarmu da bil Adama.”

Yayin da yake taya al’ummar Musulmi murnar zagayowar Idi, Shugaba Buhari ya shawarci Musulmi da su “Kyautata kyawawan dabi’un Musulunci ta hanyar misalai da kuma aiki da su,” ya kara da cewa, “Musulmi su guji cudanya da muggan ra’ayoyin masu tsattsauran ra’ayi da suka yi wa Musulunci mummunar fahimta.”

Dangane da kalubalen tsaro da tsadar rayuwa a kasar, shugaba Buhari ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa “ba zan huta ba har sai na kawo wa ‘yan Nijeriya sauki,” ya kara da cewa “na san matsalolin da mutane ke fuskanta kuma ina kokarin magance su. .”

Ya kuma ba da bayani na musamman ga jami’an tsaro da ke yaki da ta’addanci ta bangarori da dama da iyalansu, da kuma garkuwa da mutane da ‘yan ta’adda suka yi garkuwa da su.

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Izzar So

Masana’antar Kannywood Ta Girgiza Da Rasuwar Daraktan ‘Izzar So’

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.