ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Na Karbar Sakamakonsu Da Hannun Hagu A Wajen Tinubu – Atiku

by Sani Anwar
1 month ago
Atiku

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa Atiku Abubakar, ya yaba wa ‘yan Nijeriya kana bin da ya bayyana a matsayin masu hakuri da juriya, wadanda kuma suke cikin mawuyacin hali ta fuskar zamantakewa da bangaren tattalin arziki.

A sakonsa na ranar samun ‘yancin kai ga ‘yan Nijeriya, jagoran ‘yan adawar ya yi zargin cewa; APC mai mulki a halin yanzu, ta yi watsi da ‘yan Nijeriya tare da makomarsu.

  • Manyan Jami’an Kasashen Afirka Suna Fatan Fadada Hadin Gwiwa Da Kasar Sin
  • Xi Ya Taya Jami’ar Tianjin Murnar Cika Shekaru 130 Da Kafuwa

Atiku ya koka da yadda ‘yan Nijeriya ke fama da radadin matsalar rashin tsaro, karuwar karancin abinci. rashin aikin yi da kuma rashin sa da samun wani ci gaba ko sauyin da zai canja wa ‘yan kasar rayuwar, illa fargaba da rashin tabbas da ke karuwa sakamakon rashin kulawar gwamnatin ta APC.

ADVERTISEMENT

“Abin takaici ne a ce, a kasar da take da dimbin arzikin yawan al’umma da dukiyoyi, amma an mayar da miliyoyin mutanenmu ‘yan gudun hijira da barace-barace a kasarsu, duk gwamnatin da ta san abin da take yi, ta kuma san hakkin al’ummar da take mulka, tana kula da jin dadi da kuma tsaron wannan al’umma tare da ba shi muhimmanci a kan komai.”

“Abin da muke fuskanta a halin yanzu shi ne, yadda gwamnati ta yi watsi da al’ummarta, yunwa na kashe ‘yan Nijeriya, ‘yan bindiga na kashe al’umma, amma duk da haka; Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu da sauran jami’an gwamnatinsa, sun zura idanu, ba tare da daukar matakin da ya dace ba.”

LABARAI MASU NASABA

NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

Yayin da yake kira ga ‘yan kasa kan cewa, kada su karaya ko fitar da rai daga rabo, Atiku ya tunatar da ‘yan Nijeriya cewa; shekarar 2027, wata dama ce da za a iya amfani da ita wajen kawar da wannan mulki na zalunci, domin tabbatar da ganin gobenmu ta yi kyau.

“Babban kyawun demokuradiyya shi ne, ‘yancin samun damar kada kuri’a, duk wadanda ake zalunta; musamman mutanenmu a halin da ake ciki yanzu, za su samu damar kawar da wannan azzalumar gwamnati a zabe mai zuwa. Babu shakka, wannan shi ne ikon da babu wani dan takara da zai iya kwacewa daga al’umma,” in ji shi.

Atiku ya kara da cewa, a shekara 65; Nijeriya ta kasance kasa wadda ke cikin wani yanayi da ya yi kama da mai tafiya a cikin yimbu, sakamakon rashin shugabanci tsawon shekaru da dama da kuma almundahana da ta dabaibaye kasar.

Sai dai, ya bukaci ‘yan Nijeriya su ci gaba da kasancewa cikin kyakkyawan fata da kuma sa ran samun canji nagari a kowane irin lokaci, yana mai jaddada cewa; idan aka samu shugabanci nagari, kasar za ta iya canzawa daga yadda take zuwa wani yanayi mai ban sha’awa da ake iya gani tattare da wasu sauran kasashe.

Shugaban ‘yan adawar, ya kuma yi wa ‘yan Nijeriya kyakkyawan fatan murnar cika shekara 65 da samun ‘yancin kai, da kuma fatan samun zaman lafiya da dorewar tattalin arziki baki-daya

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane
Labarai

NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane

November 13, 2025
Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle
Labarai

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

November 13, 2025
Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

November 13, 2025
Next Post
Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taba Yi

Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taba Yi

LABARAI MASU NASABA

NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane

NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane

November 13, 2025
Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25

Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25

November 13, 2025
Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu

Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu

November 13, 2025
Nijeriya Za Ta Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Gusau

Nijeriya Za Ta Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Gusau

November 13, 2025
‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026

‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026

November 13, 2025
Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

November 13, 2025
Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

November 13, 2025
Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

November 13, 2025
Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.