• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Sun Fara Nadamar Zaben Tinubu – Shugaban PDP Na Ondo

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
‘Yan Nijeriya Sun Fara Nadamar Zaben Tinubu – Shugaban PDP Na Ondo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babbar jam’iyyar adawa ta PDP ta bayyana cewa a yanzu haka ‘yan Nijeriya wadanda suka zabi Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu suna nadama.

Shugaban jam’iyyar PDP a Jihar Ondo, Fatai Adams, ya bayyana hakan ne a wata sanarwa dauke da sa hannun sakataren yada labaran jam’iyyar, Kennedy Peretei da ya fitar birnin Akure.

  • Muna Bibiyar Masu Juyin Mulkin Nijar, Mu Ga Iya Gudun Ruwansu – Tinubu

A cewar jam’iyyar, ‘yan watannin da shugaban ya yi a kan karagar mulki ya kara ingiza ‘yan Nijeriya a cikin mawuyacin hali na tsadar rayuwa da ba a taba ganin irinsa ba.

Adams wanda ke mayar da martani ga shugaban jam’iyyar APC mai mulki a Jihar Ondo, Ade Adetimehin, wanda ya ce jam’iyyar PDP ta fada cikin rudani.

Ya ce a maimakon jam’iyyar APC da gwamnatinta su mayar da hankali kan mawuyacin halin da suka jefa ‘yan Nijeriya a ciki na tsawaon shakara 8 da suka yi a kan karagar mulki, sai suka kama wani abu daban.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

A cewarsa, “Kila Adetimehin shi ne kadai mutumin da ya manta da cewa, al’ummar Jihar Ondo suna sane cewa jam’iyyarsa ta APC ita ce silar da ta jefa mutane cikin wannan mawuyacin halin da suke ciki a halin yanzu, musamman ma lokacin da aka cire tallafin mai.

“Bai fahimci lamarin ba, wanda hatta wadanda aka yaudare su su zabi APC a 2023, tuni sun yi nadama tare da kokawa da yadda kuskuransu suka jawo wa kansu da iyalansu wahala.

“Irin wannan mutum idan yana da kunya ya kamata ya durkusa ya roki al’umma kan babbar masifar da jam’iyyarsa ta jefa mutane.

“Har yana iya bude bakinsa ya ce PDP ta mutu, wannan ai abun dariya ne.
Da yake mayar da martani game da sauya shekar ‘ya’yan PDP zuwa jam’iyya mai mulki a jihar, Adams ya ce “Mafi rinjayen kansilolin 203 da Adetimehin ke bikin shiga jam’iyyarsa ba su taka rawar gani ba a zabukan da suka gabata a Jihar Ondo.

“Kadan daga cikinsu sun kasance a APC tun 2016. A bayyana yake yadda suka sauya sheka zuwa PDP haka suka koma APC, amma ba kowa ne zai iya fahimtar ba, musamman Adetimehin da ke shugabantar jam’iyyar APC mai cike da hadari a jihar, ya kamata ya daina yaudarar kansa.

“Jam’iyyar PDP a Jihar Ondo ta rabauta da wasu ‘yan tsiraru da ke cikin halin kaka-ni-ka-yi a cikin jirgin Adetimehin na APC da ya nutse.

“Yayin da muke tausaya wa irin wadannan mutane, abin takaici ne wadanda ya kamata su yi kuka suna rawa da murna.
“Amma ba da dadewa ba, gaskiyar za ta bayyana a kansu cewa lalle sun kasance makarya”.

Shugaban jam’iyyar ya bayyana cewa PDP ba ta durkushe ba, kuma hakan ba zai taba faruwa ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCPDP
ShareTweetSendShare
Previous Post

Taron Kolin BRICS Zai Ingiza Daidaito Da Karsashi Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Tashina

Next Post

Abba Da Ganduje Sun Yi Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Yakubu Wakilin Jaridar Leadership Na Kano

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

2 weeks ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

2 weeks ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

2 weeks ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

3 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

3 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

3 weeks ago
Next Post
Abba Da Ganduje Sun Yi Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Yakubu Wakilin Jaridar Leadership Na Kano

Abba Da Ganduje Sun Yi Ta'aziyyar Rasuwar Abdullahi Yakubu Wakilin Jaridar Leadership Na Kano

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

September 19, 2025
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

September 19, 2025
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

September 19, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Tinubu

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.