ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Bibiyar Masu Juyin Mulkin Nijar, Mu Ga Iya Gudun Ruwansu – Tinubu

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Juyin Mulkin Nijar
  • …Nijeriya Na Da Karfin Tuwon Maido Bazoum Cikin Sa’o’i 24 -Dakta Blessing
  • …Dattawan Arewa Sun Sake Rokon A Dage Wa Kasar Takunkumai

Shugaban Nijeriya kuma shugaban Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS), Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa suna bibiyar sojojin da suka yi junyin mulki a Nijar su ga iya gudun ruwansu.

Tinubu ya ce ECOWAS ba za ta lamunci gwamnatin soja ba a daidai lokacin da ake mulkin dimokuradiyya.

Ya jinjina wa kungiyar raya tattalin arzikin kasashen tsakiyar Afirka (ECCAS) bisa irin gudunmuwar da suke bayarwa kan batun juyin mulkin kasar Nijar.

ADVERTISEMENT

Tinubu ya bayyana hakan ne a lokacin da ya karbi bakancin wakilin Shugaban Ali Bongo Ondimba kuma ministan harkokin wajen kasar Gabon, Mista Hermann Immongault, a fadar gwamnati da ke Abuja ranar Talata.

Shugaban ya kara da cewa sakon na musamman na goyon baya da hadin kai daga Shugaba Bongo, wanda ya zama shugaban ECCAS, yana mai bayyana cikakken goyon bayan kudurorin ECOWAS kan juyin mulki a Nijar, ya kara tabbatar da cewa juyin mulkin sojoji a daidai lokacin da ake mulkin dimokuradiyya ba abu ne da za a amince da shi ba a Nahiyar Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

“Ina godiya da irin hadin kai da goyon bayan da Shugaba Bongo ya bayar kan halin da ake ciki a Nijar. Muna kokarin yadda za a warware lamarin cikin ruwan sanyi ba tare da matsala ba. Muna da mutane masu yawa da ke shiga tsakani.

“Na fahimci tsoron da mutanenmu ke yi kan kowane irin matakin soja. Muna aiki don kiyaye takunkumin da aka kakaba kuma muna bin su domin mu ga iya gudun ruwansu.

“Muna farin cikin sanin cewa ECCAS na tare da mu a kan wannan lamari. ECOWAS ba za ta amince da mulkin soja ba a daidai lokacin da ake mulkin dimokuradiyya,” in ji shi.

…Nijeriya Na Da Karfin Tuwon Maido Bazoum Cikin Sa’o’i 24 -Dakta Blessing

Har iya yau, wata kwararriyar masaniyar harkokin tsaro, Dakta Blessing Agbomhere ta bayyana cewa Nijeriya a karkashin Shugaban Kasa Tinubu kuma shugaban ECOWAS na da karfin tuwon maido da hambararren Shugaban Kasan Nijar, Mohammed Bazoum kan kujera Cikin sa’o’i 24.

Agbomhere ta bayyana kaduwarta da takaicin yadda wasu ‘yan Nijeriya ke nuna adawa da shirin ECOWAS na mayar da mulkin farar hula a Jamhuriyar Nijar.

A cewarta, fargabar da wasu ‘yan Nijeriya ke nunawa kan shiri da rundunar sojin kasar ke yi na tunkarar gwamnatin sojojin juyin mulkin Nijar cikin kankanin lokaci lamari ne da ke nuni da rashin kishin kasa da kuma kin daukar matakin da ya dace daga gwamnatin da ta shude wacce tun farko ta yi fafutuka wajen dakile ’yan ta’adda da ‘yan bidiga da suka addabi wasu sassan kasar nan.

Ta jaddada cewa ba gaskiya ba ne da ake cewa nuna irin halin da sojojin Nijeriya a karkashin jagorancin Shugaba Tinubu ke ciki, wanda ya yi imanin cewa yana da dukkanin bayanai da dabarun da ake bukata don gudanar da aiki cikin gaggawa da samun nasara a Nijar ba tare da bata lokaci ba da kuma haifar da hasarar da ba gaira ba dalili ga sojojin kasar.

“Shugaba Tinubu ya shirya tsaf don sake dawo da martabar Nijeriya, dole ne mu mara masa baya don sake mayar da Nijeriya matsayinta na jagoran kasashen Afirka “, in ji shi.

Sai dai ta bayyana cewa tattaunawa ita ce hanya mafi dacewa wajen warware rikicin siyasa a Nijar, tana mai jaddada cewa bai kamata Nijeriya ta yi watsi da alhakkin da ya rataya a wuyanta na wanzar da mulkin dimokuradiyya a yankin Afirka ta yamma ba, ta hanyar daukar matakan soja, kamar irin rawar da ta taka a tsawon shekaru a kasashen Laberiya da Sao Tome da Sierra Leone da Cote D’Iboire, sannan za ta ci gaba da taka rawa wajen kare martabar mulkin dimokuradiyya da zaman lafiya a yankin.

 

…Dattawan Arewa Sun Sake Rokon A Dage Wa Kasar Takunkumai

Sai dai kuma kungiyar dattawan arewa (NEF) ta sake shawarci Shugaba Tinubu wanda shi ne shugaban ECOWAS ya gaggauta dage wa kasar Nijar takunkumai da aka kakaba mata.

A dai ranar 4 ga Agusta ce, Nijeriya ta rufe dukkan iyakokinta da kasar Nijar da kuma yanke wutar lantarki sakamakon kin mayar da mulki ga hambararren shugaban kasan, Bazoum da sojojin juyin mulki suka hambarar da gwamnatinsa a ranar 26 ga Yuli.

Da yake jawabi a taron manema labarai a Abuja, Daraktan yada labarai da hulda da jama’a na kungiyar NEF, Dakta Hakeem Baba Ahmed, ya ce, “Ya kamata Nijeriya ta cire duk wani takunkumi da sauran matakan da ta dauka na tilasta wa gwamnatin sojojin juyin mulki.”

Ya bukaci Tinubu da ya tabbatar da tsaron lafiyar hambararren shugaban kasan, Bazoum da iyalansa da kuma maido da tsarin mulkin dimokuradiyya, su kasance muhimman abubuwan tattaunawa.

Kungiyar NEF ta yi watsi da amfani da karfin soja a kasar, inda ta kara da cewa matakin zai kara dagula lamarin ne kawai.

“Ya kamata a yi watsi da amfani da karfin soja a kan Nijar. Da wuya a cimma manufofin maido da tsarin mulkin dimokuradiyya idan aka yi amfani da karfin soja. Hakan zai kara dagula lamarin tsaro da ke addabar al’ummar yankin kasashen ECOWAS,” in ji shi.

Juyin Mulkin Nijar
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Next Post
Ruftawar Masallacin Fadar Zazzau: Abubuwan Da Suka Kamata A Sani Na Tarihi

Ruftawar Masallacin Fadar Zazzau: Abubuwan Da Suka Kamata A Sani Na Tarihi

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.