• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Sun Fara Nadamar Zaben Tinubu – Shugaban PDP Na Ondo

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
‘Yan Nijeriya Sun Fara Nadamar Zaben Tinubu – Shugaban PDP Na Ondo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babbar jam’iyyar adawa ta PDP ta bayyana cewa a yanzu haka ‘yan Nijeriya wadanda suka zabi Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu suna nadama.

Shugaban jam’iyyar PDP a Jihar Ondo, Fatai Adams, ya bayyana hakan ne a wata sanarwa dauke da sa hannun sakataren yada labaran jam’iyyar, Kennedy Peretei da ya fitar birnin Akure.

  • Muna Bibiyar Masu Juyin Mulkin Nijar, Mu Ga Iya Gudun Ruwansu – Tinubu

A cewar jam’iyyar, ‘yan watannin da shugaban ya yi a kan karagar mulki ya kara ingiza ‘yan Nijeriya a cikin mawuyacin hali na tsadar rayuwa da ba a taba ganin irinsa ba.

Adams wanda ke mayar da martani ga shugaban jam’iyyar APC mai mulki a Jihar Ondo, Ade Adetimehin, wanda ya ce jam’iyyar PDP ta fada cikin rudani.

Ya ce a maimakon jam’iyyar APC da gwamnatinta su mayar da hankali kan mawuyacin halin da suka jefa ‘yan Nijeriya a ciki na tsawaon shakara 8 da suka yi a kan karagar mulki, sai suka kama wani abu daban.

Labarai Masu Nasaba

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

A cewarsa, “Kila Adetimehin shi ne kadai mutumin da ya manta da cewa, al’ummar Jihar Ondo suna sane cewa jam’iyyarsa ta APC ita ce silar da ta jefa mutane cikin wannan mawuyacin halin da suke ciki a halin yanzu, musamman ma lokacin da aka cire tallafin mai.

“Bai fahimci lamarin ba, wanda hatta wadanda aka yaudare su su zabi APC a 2023, tuni sun yi nadama tare da kokawa da yadda kuskuransu suka jawo wa kansu da iyalansu wahala.

“Irin wannan mutum idan yana da kunya ya kamata ya durkusa ya roki al’umma kan babbar masifar da jam’iyyarsa ta jefa mutane.

“Har yana iya bude bakinsa ya ce PDP ta mutu, wannan ai abun dariya ne.
Da yake mayar da martani game da sauya shekar ‘ya’yan PDP zuwa jam’iyya mai mulki a jihar, Adams ya ce “Mafi rinjayen kansilolin 203 da Adetimehin ke bikin shiga jam’iyyarsa ba su taka rawar gani ba a zabukan da suka gabata a Jihar Ondo.

“Kadan daga cikinsu sun kasance a APC tun 2016. A bayyana yake yadda suka sauya sheka zuwa PDP haka suka koma APC, amma ba kowa ne zai iya fahimtar ba, musamman Adetimehin da ke shugabantar jam’iyyar APC mai cike da hadari a jihar, ya kamata ya daina yaudarar kansa.

“Jam’iyyar PDP a Jihar Ondo ta rabauta da wasu ‘yan tsiraru da ke cikin halin kaka-ni-ka-yi a cikin jirgin Adetimehin na APC da ya nutse.

“Yayin da muke tausaya wa irin wadannan mutane, abin takaici ne wadanda ya kamata su yi kuka suna rawa da murna.
“Amma ba da dadewa ba, gaskiyar za ta bayyana a kansu cewa lalle sun kasance makarya”.

Shugaban jam’iyyar ya bayyana cewa PDP ba ta durkushe ba, kuma hakan ba zai taba faruwa ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCPDP
ShareTweetSendShare
Previous Post

Taron Kolin BRICS Zai Ingiza Daidaito Da Karsashi Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Tashina

Next Post

Abba Da Ganduje Sun Yi Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Yakubu Wakilin Jaridar Leadership Na Kano

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

3 hours ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

4 hours ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

5 days ago
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Tambarin Dimokuradiyya

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

7 days ago
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

1 week ago
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

1 week ago
Next Post
Abba Da Ganduje Sun Yi Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Yakubu Wakilin Jaridar Leadership Na Kano

Abba Da Ganduje Sun Yi Ta'aziyyar Rasuwar Abdullahi Yakubu Wakilin Jaridar Leadership Na Kano

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.