• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Sanda Da ‘Yan Kasuwa Sun Yi Hadin Guiwa Don Kawo Karshen Kwacen Waya A Kano

by Sadiq
3 years ago

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta hada hannu da kungiyar kasuwar hada-hadar wayoyin hannu ta jihar domin dakile matsalar sace-sace da kwace waya da ya addabi kwayar birnin jihar.

Kwamishinan ‘yan sandan Kano, Sama’ila Dikko, ne ya tabbatar da hakan a lokacin da kungiyar ta kai masa ziyara da kuma ba shi lambar girma a ofishinsa.

  • Farashin Alkama Ya Sauka a Duniya
  • Kotu Ta Dage Shari’ar Wanda Ake Zargi Da Auran Jikarsa A Zamfara 

Kwamishinan ya ce ya yi matukar farin ciki bisa yadda kungiyar ta yi kudirin hada hannu da rundunar domin ganin an dakile ta’adar sace-sacen wayoyi, musamman a wannan lokaci da lamarin ya addabi al’ummar jihar Kano.

Samaila Dikko, ya ce kofarsu a bude take wajen yin mu’amala da kungiyar duba da yawan kasuwannin siyar da wayoyin da ke Kano, inda ya ce kungiyar za ta taka rawar gani wajen zakulo bata-garin ta hanyoyi daban-daban.

Tun da fari, a jawabinsa shugaban gamayyar kungiyoyin hada-hadar wayoyin hannu ta jihar Kano, Alhaji Ahmad Tijjani Usman, ya ce Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, ya gayyaci kungiyar domin tattauna wa da ita kan zargin da ake yi wa ‘yan kasuwar wayoyin hannu.

LABARAI MASU NASABA

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

ya ce ana zargin ana hada kai da masu sayar da wayoyin domin sayar da wayoyin da aka sato ko kwato, inda ya ce ya ce wannan zargi ba haka ya ke ba domin suma suna iya bakin kokarisu don ganin basu sayi wayar da aka sato ko aka kwato ba.

Shugaban kungiyar ya bayyana cewa za su ba da gudunmawarsu don kawar da wannan dabi’a da matasa ke yi a fadin jihar.

Shugaban ya ce kungiyar ta samar da cikakken kwamiti na musamman domin bibiyar masu shigo wa kasuwannin wayoyin hannu domin sayar da wayoyin da suka kwata ko sata domin Idan ba a sayen wayoyin dole barayin su daina satowa.

Ya kuma ba da lambobin karta-kwana ga duk wanda a ka sace wa ko kwace wa waya domin gano wadanda su ka aikata cikin gaggawa.

Lambobin sune ;08065416459 ko 08039725508 ko kuma [email protected].

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati
Labarai

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba
Labarai

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta
Manyan Labarai

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Next Post
Zaben Fid Da Gwani: Lawan, Akpabio Da Tambuwal Na Iya Fuskantar Daurin Shekara Biyu -Lauya

Zaben Fid Da Gwani: Lawan, Akpabio Da Tambuwal Na Iya Fuskantar Daurin Shekara Biyu -Lauya

LABARAI MASU NASABA

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.