ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Dage Shari’ar Wanda Ake Zargi Da Auran Jikarsa A Zamfara 

by Hussein Yero
4 years ago
Kotu

Wata babbar kotun shari’a Musulunci da ke karamar hukumar Tsafe a jihar Zamfara, ta dage ci gaba da sauraron karar da aka shigar kan wani mutum da ake zargi da auren jikansa.

Alkalin kotun, Malam Bashir Mahe, ya dage ci gaba da sauraren karar domin bai wa lauyan wanda ake kara, Abubakar Ayuba, damar yin nazari kan tuhume-tuhumen da ake yi wa wanda yake karewa.

  • Kotu Ta Yanke Wa Matashi Hukuncin Sharar Titi Da Bulala 12 A Kano
  • Ban Taba Goyon Bayan Tinubu Don Ya Zabe Ni A Matsayin Mataimakinsa Ba – Shettima

Hukumar Hisbah ce ta shigar da karar, inda take neman a warware auren da aka daura shekara 20 da ta gabata.

ADVERTISEMENT

Hisbah ta shaida wa kotun cewa, auren da aka yi tsakanin Malam Musa Dangote da Wasila Musa ‘yar yayansa, ya saba wa dokokin shari’a da kuma tsarin shari’ar Musulunci.

Hukumar ta ce ta shigar da kara a kan ma’auratan ne bayan kokarin da Majalisar Shawarar Malaman addinin musulunci (Shura) da Masarautar Tsafe suka yi na ganin abun bai je kotu ba abi maslahar abun ya ci tura, inda magidanci ya ce ba za ta sabu bindiga a ruwa ba.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Lauyan hukumar Malam Sani Muhammad, ya shaida wa kotun cewa binciken da hukumomin addinin musulunci daban-daban da masarautar suka yi ya nuna cewa ma’auratan da suka yi aure a 1999 suna da alaka kai tsaye ta jini don haka ya haramta aure a tsakaninsu.

Muhammad ya ce, matakin ya saba wa koyarwar addanin Musulunci kamar yadda ya zo a cikin Alkur’ani sura uku aya ta 23.

Don haka ya roki kotu da ta gaggauta yanke auren.

A halin da ake ciki, Ayuba, ya musanta zarge-zargen kuma ya bukaci samun damar bin rahoton binciken hukumar da ta gabatar a matsayin shaida.

Ayuba ya kuma bukaci a ba shi lokaci domin nazarin tuhumar da kuma shirya kariya.

Alkalin kotun ya bayar da umarnin mika rahoton binciken hukumar ga lauyan da ke kare wadanda ake kara sannan, ya ba shi kwanaki biyar ya yi nazari tare da bayar da amsa gamsasa a gaban kotu.

Daga nan ne alkalin ya dage zaman domin ci gaba da sauraren karar zuwa ranar Litinin mai zuwa.

Wakilinmu ya ruwaito cewa Musa mai shekaru 35 ya haifi ‘ya’ya takwas a cikin auren shekara 20 da suka yi, don yanzu haka ake neman warware shi.

Kotu
Hussein Yero
+ postsBio
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero-2/
    Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Ƙaddamar Da Jakadun Wayar Da Kai Game Da Rigakafi
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero-2/
    Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero-2/
    Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero-2/
    Ramadan: Hon Jaji Ya Ƙaddamar Da Tallafin Abinci Ga Mutane Sama Da 500,000 A Zamfara

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Akwai Kwanciyar Hankalin Yin Kasuwanci A Nijeriya — Lai Mohammed

Akwai Kwanciyar Hankalin Yin Kasuwanci A Nijeriya — Lai Mohammed

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.