ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 22, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Dage Shari’ar Wanda Ake Zargi Da Auran Jikarsa A Zamfara 

by Hussein Yero
4 years ago
Kotu

Wata babbar kotun shari’a Musulunci da ke karamar hukumar Tsafe a jihar Zamfara, ta dage ci gaba da sauraron karar da aka shigar kan wani mutum da ake zargi da auren jikansa.

Alkalin kotun, Malam Bashir Mahe, ya dage ci gaba da sauraren karar domin bai wa lauyan wanda ake kara, Abubakar Ayuba, damar yin nazari kan tuhume-tuhumen da ake yi wa wanda yake karewa.

  • Kotu Ta Yanke Wa Matashi Hukuncin Sharar Titi Da Bulala 12 A Kano
  • Ban Taba Goyon Bayan Tinubu Don Ya Zabe Ni A Matsayin Mataimakinsa Ba – Shettima

Hukumar Hisbah ce ta shigar da karar, inda take neman a warware auren da aka daura shekara 20 da ta gabata.

ADVERTISEMENT

Hisbah ta shaida wa kotun cewa, auren da aka yi tsakanin Malam Musa Dangote da Wasila Musa ‘yar yayansa, ya saba wa dokokin shari’a da kuma tsarin shari’ar Musulunci.

Hukumar ta ce ta shigar da kara a kan ma’auratan ne bayan kokarin da Majalisar Shawarar Malaman addinin musulunci (Shura) da Masarautar Tsafe suka yi na ganin abun bai je kotu ba abi maslahar abun ya ci tura, inda magidanci ya ce ba za ta sabu bindiga a ruwa ba.

LABARAI MASU NASABA

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

Lauyan hukumar Malam Sani Muhammad, ya shaida wa kotun cewa binciken da hukumomin addinin musulunci daban-daban da masarautar suka yi ya nuna cewa ma’auratan da suka yi aure a 1999 suna da alaka kai tsaye ta jini don haka ya haramta aure a tsakaninsu.

Muhammad ya ce, matakin ya saba wa koyarwar addanin Musulunci kamar yadda ya zo a cikin Alkur’ani sura uku aya ta 23.

Don haka ya roki kotu da ta gaggauta yanke auren.

A halin da ake ciki, Ayuba, ya musanta zarge-zargen kuma ya bukaci samun damar bin rahoton binciken hukumar da ta gabatar a matsayin shaida.

Ayuba ya kuma bukaci a ba shi lokaci domin nazarin tuhumar da kuma shirya kariya.

Alkalin kotun ya bayar da umarnin mika rahoton binciken hukumar ga lauyan da ke kare wadanda ake kara sannan, ya ba shi kwanaki biyar ya yi nazari tare da bayar da amsa gamsasa a gaban kotu.

Daga nan ne alkalin ya dage zaman domin ci gaba da sauraren karar zuwa ranar Litinin mai zuwa.

Wakilinmu ya ruwaito cewa Musa mai shekaru 35 ya haifi ‘ya’ya takwas a cikin auren shekara 20 da suka yi, don yanzu haka ake neman warware shi.

Kotu
Hussein Yero
+ postsBio
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero-2/
    Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Ƙaddamar Da Jakadun Wayar Da Kai Game Da Rigakafi
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero-2/
    Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero-2/
    Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero-2/
    Ramadan: Hon Jaji Ya Ƙaddamar Da Tallafin Abinci Ga Mutane Sama Da 500,000 A Zamfara

MASU ALAKA

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta
Labarai

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

July 21, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC
Labarai

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

July 21, 2026
Next Post
Akwai Kwanciyar Hankalin Yin Kasuwanci A Nijeriya — Lai Mohammed

Akwai Kwanciyar Hankalin Yin Kasuwanci A Nijeriya — Lai Mohammed

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa

Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa

July 21, 2026
Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa

Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa

July 21, 2026
Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao

Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao

July 21, 2026
An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026

An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026

July 21, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

July 21, 2026
Li Qiang Ya Taya Andy Burnham Murnar Zama Sabon Firaministan Birtaniya

Li Qiang Ya Taya Andy Burnham Murnar Zama Sabon Firaministan Birtaniya

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida

Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida

July 21, 2026
Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule

Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule

July 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.