ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Dage Shari’ar Wanda Ake Zargi Da Auran Jikarsa A Zamfara 

by Hussein Yero
4 years ago
Kotu

Wata babbar kotun shari’a Musulunci da ke karamar hukumar Tsafe a jihar Zamfara, ta dage ci gaba da sauraron karar da aka shigar kan wani mutum da ake zargi da auren jikansa.

Alkalin kotun, Malam Bashir Mahe, ya dage ci gaba da sauraren karar domin bai wa lauyan wanda ake kara, Abubakar Ayuba, damar yin nazari kan tuhume-tuhumen da ake yi wa wanda yake karewa.

  • Kotu Ta Yanke Wa Matashi Hukuncin Sharar Titi Da Bulala 12 A Kano
  • Ban Taba Goyon Bayan Tinubu Don Ya Zabe Ni A Matsayin Mataimakinsa Ba – Shettima

Hukumar Hisbah ce ta shigar da karar, inda take neman a warware auren da aka daura shekara 20 da ta gabata.

ADVERTISEMENT

Hisbah ta shaida wa kotun cewa, auren da aka yi tsakanin Malam Musa Dangote da Wasila Musa ‘yar yayansa, ya saba wa dokokin shari’a da kuma tsarin shari’ar Musulunci.

Hukumar ta ce ta shigar da kara a kan ma’auratan ne bayan kokarin da Majalisar Shawarar Malaman addinin musulunci (Shura) da Masarautar Tsafe suka yi na ganin abun bai je kotu ba abi maslahar abun ya ci tura, inda magidanci ya ce ba za ta sabu bindiga a ruwa ba.

LABARAI MASU NASABA

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Lauyan hukumar Malam Sani Muhammad, ya shaida wa kotun cewa binciken da hukumomin addinin musulunci daban-daban da masarautar suka yi ya nuna cewa ma’auratan da suka yi aure a 1999 suna da alaka kai tsaye ta jini don haka ya haramta aure a tsakaninsu.

Muhammad ya ce, matakin ya saba wa koyarwar addanin Musulunci kamar yadda ya zo a cikin Alkur’ani sura uku aya ta 23.

Don haka ya roki kotu da ta gaggauta yanke auren.

A halin da ake ciki, Ayuba, ya musanta zarge-zargen kuma ya bukaci samun damar bin rahoton binciken hukumar da ta gabatar a matsayin shaida.

Ayuba ya kuma bukaci a ba shi lokaci domin nazarin tuhumar da kuma shirya kariya.

Alkalin kotun ya bayar da umarnin mika rahoton binciken hukumar ga lauyan da ke kare wadanda ake kara sannan, ya ba shi kwanaki biyar ya yi nazari tare da bayar da amsa gamsasa a gaban kotu.

Daga nan ne alkalin ya dage zaman domin ci gaba da sauraren karar zuwa ranar Litinin mai zuwa.

Wakilinmu ya ruwaito cewa Musa mai shekaru 35 ya haifi ‘ya’ya takwas a cikin auren shekara 20 da suka yi, don yanzu haka ake neman warware shi.

Kotu
Hussein Yero
+ postsBio
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero-2/
    Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Ƙaddamar Da Jakadun Wayar Da Kai Game Da Rigakafi
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero-2/
    Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero-2/
    Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero-2/
    Ramadan: Hon Jaji Ya Ƙaddamar Da Tallafin Abinci Ga Mutane Sama Da 500,000 A Zamfara

MASU ALAKA

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
Labarai

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Next Post
Akwai Kwanciyar Hankalin Yin Kasuwanci A Nijeriya — Lai Mohammed

Akwai Kwanciyar Hankalin Yin Kasuwanci A Nijeriya — Lai Mohammed

LABARAI MASU NASABA

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.