ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Fid Da Gwani: Lawan, Akpabio Da Tambuwal Na Iya Fuskantar Daurin Shekara Biyu -Lauya

by Muhammad Maitela
4 years ago
Lawan

Akwai yiwuwar Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Ahmad Lawan da tsohon gwamnan Jihar Akwa Ibom, Godswill Akpabio da Gwaman Jihar Sakwato, Aminu Waziri Tambuwal da sauran ‘yan takarar wadanda suka sa yi tikitin takara fiye da daya su fuskanci hukuncin daurin shekara biyu a gidan yari a karkashin dokar zabe ta 2022.

Wannan furucin ya fito ne daga bakin Kwamishinan Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta na Jihar Akwa Ibom, Mista Mike Igini a wata fira da ya gudanar tare da gidan talabijin Channels ranar Talata da ta gabata. Inda ya jingina hujjarsa da sashe na 115 (D) na dokar zabe ta 2022.
Ya kara da cewa, “Saboda haka duk wanda ya yi kuskuren sanya hannu ga fom din neman yin takara a yanki /shiyya ko na sakamako fiye da daya a lokacin guda, ya aikata laifi kuma wanda yana iya kai ga yanke masa hukuncin daurin shekara a kalla biyu gidan kaso.

  • Abin Da Yasa Ba Mu Buga Sunan Lawan Da Akpabio Ba – INEC

Mista Igini ya yi karin haske kan abin da yake nufi da “yanki/ shiyya” a matsayin kalmar da hukumar zabe kan yi amfani da ita, wadda take nufin tsayawa takara biyu a lokaci guda, wanda ya hada da na shugaban kasa ne, na gwamna, sanata ko majalisar wakilai tare da na majalisar dokokin jiha.

ADVERTISEMENT

A hannu guda kuma, ya ce duk dan takarar da ya yi wa wannan dokar hawan kawara zai fuskanci hukuncin daurin shekara biyu gidan yari. Ya ce dokar tana nan a sashe na 115 (3), wanda ta shafi hatta a jihohi ga masu yunkurin mallakar fam din takara guda biyu a lokaci guda, hakan yi wa doka karan-tsaye ne.

Ya ce Mista Akpabio ya tsaya takarar shugaban kasa ne a karkashin jam’iyyar APC, wanda daga bisani ya janye a ranar 7 ga watan Yuni tare da bayyana wa magoya bayansa su zabi Asiwaju Bola Tinubu, wanda ya lashe zaben takarar shugaban kasa a APC.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Baya ga zaben fid da gwani na shugaban kasa, ranar 27 ga watan Mayu, Udom Ekpoudom, tsohon mataimakin safeto Janar na ‘yansanda, ya samu nasarar lashe zaben sanata a shiyyar arewa maso yammacin Jihar Akwa Ibom.

Shi kuma Sanata Lawan bayan ya sha kasa a zaben fid da gwani da jam’iyyar APC ta gudanar na shugaban kasa, wasu bayanai sun nuna ya nemi Bashir Machina, wanda ya samu nasarar lashe zaben arewacin Yobe ya janye masa.

Ya ce bisa hakan ya nuna cewa shugaban majalisar dattawan Nijeriya da Mista Akpabio wata kila a boye sun mallaki fom din takarar kujerar sanata a yankunansu, alhalin kuma a hannu guda suna neman takarar kujerar shugaban kasa.

Mista Igini bai tsaya nan ba, ya lissafo karin wasu ‘yan siyasar da suka bi ta kan wannan doka, wadanda suka hada da Gwamna Ben Ayade na Jihar Kuros Ribas, Tambuwal tare da Bala Mohammed na Jihar Bauchi.

Lawan
Muhammad Maitela
+ postsBio
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Kashe Kansila A Adamawa

'Yan Bindiga Sun Kashe Kansila A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.