• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Fid Da Gwani: Lawan, Akpabio Da Tambuwal Na Iya Fuskantar Daurin Shekara Biyu -Lauya

by Muhammad Maitela
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Zaben Fid Da Gwani: Lawan, Akpabio Da Tambuwal Na Iya Fuskantar Daurin Shekara Biyu -Lauya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akwai yiwuwar Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Ahmad Lawan da tsohon gwamnan Jihar Akwa Ibom, Godswill Akpabio da Gwaman Jihar Sakwato, Aminu Waziri Tambuwal da sauran ‘yan takarar wadanda suka sa yi tikitin takara fiye da daya su fuskanci hukuncin daurin shekara biyu a gidan yari a karkashin dokar zabe ta 2022.

Wannan furucin ya fito ne daga bakin Kwamishinan Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta na Jihar Akwa Ibom, Mista Mike Igini a wata fira da ya gudanar tare da gidan talabijin Channels ranar Talata da ta gabata. Inda ya jingina hujjarsa da sashe na 115 (D) na dokar zabe ta 2022.
Ya kara da cewa, “Saboda haka duk wanda ya yi kuskuren sanya hannu ga fom din neman yin takara a yanki /shiyya ko na sakamako fiye da daya a lokacin guda, ya aikata laifi kuma wanda yana iya kai ga yanke masa hukuncin daurin shekara a kalla biyu gidan kaso.

  • Abin Da Yasa Ba Mu Buga Sunan Lawan Da Akpabio Ba – INEC

Mista Igini ya yi karin haske kan abin da yake nufi da “yanki/ shiyya” a matsayin kalmar da hukumar zabe kan yi amfani da ita, wadda take nufin tsayawa takara biyu a lokaci guda, wanda ya hada da na shugaban kasa ne, na gwamna, sanata ko majalisar wakilai tare da na majalisar dokokin jiha.

A hannu guda kuma, ya ce duk dan takarar da ya yi wa wannan dokar hawan kawara zai fuskanci hukuncin daurin shekara biyu gidan yari. Ya ce dokar tana nan a sashe na 115 (3), wanda ta shafi hatta a jihohi ga masu yunkurin mallakar fam din takara guda biyu a lokaci guda, hakan yi wa doka karan-tsaye ne.

Ya ce Mista Akpabio ya tsaya takarar shugaban kasa ne a karkashin jam’iyyar APC, wanda daga bisani ya janye a ranar 7 ga watan Yuni tare da bayyana wa magoya bayansa su zabi Asiwaju Bola Tinubu, wanda ya lashe zaben takarar shugaban kasa a APC.

Labarai Masu Nasaba

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

Baya ga zaben fid da gwani na shugaban kasa, ranar 27 ga watan Mayu, Udom Ekpoudom, tsohon mataimakin safeto Janar na ‘yansanda, ya samu nasarar lashe zaben sanata a shiyyar arewa maso yammacin Jihar Akwa Ibom.

Shi kuma Sanata Lawan bayan ya sha kasa a zaben fid da gwani da jam’iyyar APC ta gudanar na shugaban kasa, wasu bayanai sun nuna ya nemi Bashir Machina, wanda ya samu nasarar lashe zaben arewacin Yobe ya janye masa.

Ya ce bisa hakan ya nuna cewa shugaban majalisar dattawan Nijeriya da Mista Akpabio wata kila a boye sun mallaki fom din takarar kujerar sanata a yankunansu, alhalin kuma a hannu guda suna neman takarar kujerar shugaban kasa.

Mista Igini bai tsaya nan ba, ya lissafo karin wasu ‘yan siyasar da suka bi ta kan wannan doka, wadanda suka hada da Gwamna Ben Ayade na Jihar Kuros Ribas, Tambuwal tare da Bala Mohammed na Jihar Bauchi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Sanda Da ‘Yan Kasuwa Sun Yi Hadin Guiwa Don Kawo Karshen Kwacen Waya A Kano

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe Kansila A Adamawa

Related

Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

2 days ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Tambarin Dimokuradiyya

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

2 days ago
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

2 days ago
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

3 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

3 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

4 weeks ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Kashe Kansila A Adamawa

'Yan Bindiga Sun Kashe Kansila A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

July 6, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

July 6, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

July 6, 2025
Sanata Dickson Ya BuÆ™aci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi YaÆ™i Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanata Dickson Ya BuÆ™aci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi YaÆ™i Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

July 6, 2025
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

July 6, 2025
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya ÆŠaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya ÆŠaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

July 6, 2025
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

July 6, 2025
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

July 6, 2025
Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

July 6, 2025
Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.