ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Fid Da Gwani: Lawan, Akpabio Da Tambuwal Na Iya Fuskantar Daurin Shekara Biyu -Lauya

by Muhammad Maitela
4 years ago
Lawan

Akwai yiwuwar Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Ahmad Lawan da tsohon gwamnan Jihar Akwa Ibom, Godswill Akpabio da Gwaman Jihar Sakwato, Aminu Waziri Tambuwal da sauran ‘yan takarar wadanda suka sa yi tikitin takara fiye da daya su fuskanci hukuncin daurin shekara biyu a gidan yari a karkashin dokar zabe ta 2022.

Wannan furucin ya fito ne daga bakin Kwamishinan Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta na Jihar Akwa Ibom, Mista Mike Igini a wata fira da ya gudanar tare da gidan talabijin Channels ranar Talata da ta gabata. Inda ya jingina hujjarsa da sashe na 115 (D) na dokar zabe ta 2022.
Ya kara da cewa, “Saboda haka duk wanda ya yi kuskuren sanya hannu ga fom din neman yin takara a yanki /shiyya ko na sakamako fiye da daya a lokacin guda, ya aikata laifi kuma wanda yana iya kai ga yanke masa hukuncin daurin shekara a kalla biyu gidan kaso.

  • Abin Da Yasa Ba Mu Buga Sunan Lawan Da Akpabio Ba – INEC

Mista Igini ya yi karin haske kan abin da yake nufi da “yanki/ shiyya” a matsayin kalmar da hukumar zabe kan yi amfani da ita, wadda take nufin tsayawa takara biyu a lokaci guda, wanda ya hada da na shugaban kasa ne, na gwamna, sanata ko majalisar wakilai tare da na majalisar dokokin jiha.

ADVERTISEMENT

A hannu guda kuma, ya ce duk dan takarar da ya yi wa wannan dokar hawan kawara zai fuskanci hukuncin daurin shekara biyu gidan yari. Ya ce dokar tana nan a sashe na 115 (3), wanda ta shafi hatta a jihohi ga masu yunkurin mallakar fam din takara guda biyu a lokaci guda, hakan yi wa doka karan-tsaye ne.

Ya ce Mista Akpabio ya tsaya takarar shugaban kasa ne a karkashin jam’iyyar APC, wanda daga bisani ya janye a ranar 7 ga watan Yuni tare da bayyana wa magoya bayansa su zabi Asiwaju Bola Tinubu, wanda ya lashe zaben takarar shugaban kasa a APC.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Baya ga zaben fid da gwani na shugaban kasa, ranar 27 ga watan Mayu, Udom Ekpoudom, tsohon mataimakin safeto Janar na ‘yansanda, ya samu nasarar lashe zaben sanata a shiyyar arewa maso yammacin Jihar Akwa Ibom.

Shi kuma Sanata Lawan bayan ya sha kasa a zaben fid da gwani da jam’iyyar APC ta gudanar na shugaban kasa, wasu bayanai sun nuna ya nemi Bashir Machina, wanda ya samu nasarar lashe zaben arewacin Yobe ya janye masa.

Ya ce bisa hakan ya nuna cewa shugaban majalisar dattawan Nijeriya da Mista Akpabio wata kila a boye sun mallaki fom din takarar kujerar sanata a yankunansu, alhalin kuma a hannu guda suna neman takarar kujerar shugaban kasa.

Mista Igini bai tsaya nan ba, ya lissafo karin wasu ‘yan siyasar da suka bi ta kan wannan doka, wadanda suka hada da Gwamna Ben Ayade na Jihar Kuros Ribas, Tambuwal tare da Bala Mohammed na Jihar Bauchi.

Lawan
Muhammad Maitela
+ postsBio
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

MASU ALAKA

Lawan
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Kashe Kansila A Adamawa

'Yan Bindiga Sun Kashe Kansila A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.