ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Fid Da Gwani: Lawan, Akpabio Da Tambuwal Na Iya Fuskantar Daurin Shekara Biyu -Lauya

by Muhammad Maitela
4 years ago
Lawan

Akwai yiwuwar Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Ahmad Lawan da tsohon gwamnan Jihar Akwa Ibom, Godswill Akpabio da Gwaman Jihar Sakwato, Aminu Waziri Tambuwal da sauran ‘yan takarar wadanda suka sa yi tikitin takara fiye da daya su fuskanci hukuncin daurin shekara biyu a gidan yari a karkashin dokar zabe ta 2022.

Wannan furucin ya fito ne daga bakin Kwamishinan Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta na Jihar Akwa Ibom, Mista Mike Igini a wata fira da ya gudanar tare da gidan talabijin Channels ranar Talata da ta gabata. Inda ya jingina hujjarsa da sashe na 115 (D) na dokar zabe ta 2022.
Ya kara da cewa, “Saboda haka duk wanda ya yi kuskuren sanya hannu ga fom din neman yin takara a yanki /shiyya ko na sakamako fiye da daya a lokacin guda, ya aikata laifi kuma wanda yana iya kai ga yanke masa hukuncin daurin shekara a kalla biyu gidan kaso.

  • Abin Da Yasa Ba Mu Buga Sunan Lawan Da Akpabio Ba – INEC

Mista Igini ya yi karin haske kan abin da yake nufi da “yanki/ shiyya” a matsayin kalmar da hukumar zabe kan yi amfani da ita, wadda take nufin tsayawa takara biyu a lokaci guda, wanda ya hada da na shugaban kasa ne, na gwamna, sanata ko majalisar wakilai tare da na majalisar dokokin jiha.

ADVERTISEMENT

A hannu guda kuma, ya ce duk dan takarar da ya yi wa wannan dokar hawan kawara zai fuskanci hukuncin daurin shekara biyu gidan yari. Ya ce dokar tana nan a sashe na 115 (3), wanda ta shafi hatta a jihohi ga masu yunkurin mallakar fam din takara guda biyu a lokaci guda, hakan yi wa doka karan-tsaye ne.

Ya ce Mista Akpabio ya tsaya takarar shugaban kasa ne a karkashin jam’iyyar APC, wanda daga bisani ya janye a ranar 7 ga watan Yuni tare da bayyana wa magoya bayansa su zabi Asiwaju Bola Tinubu, wanda ya lashe zaben takarar shugaban kasa a APC.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Baya ga zaben fid da gwani na shugaban kasa, ranar 27 ga watan Mayu, Udom Ekpoudom, tsohon mataimakin safeto Janar na ‘yansanda, ya samu nasarar lashe zaben sanata a shiyyar arewa maso yammacin Jihar Akwa Ibom.

Shi kuma Sanata Lawan bayan ya sha kasa a zaben fid da gwani da jam’iyyar APC ta gudanar na shugaban kasa, wasu bayanai sun nuna ya nemi Bashir Machina, wanda ya samu nasarar lashe zaben arewacin Yobe ya janye masa.

Ya ce bisa hakan ya nuna cewa shugaban majalisar dattawan Nijeriya da Mista Akpabio wata kila a boye sun mallaki fom din takarar kujerar sanata a yankunansu, alhalin kuma a hannu guda suna neman takarar kujerar shugaban kasa.

Mista Igini bai tsaya nan ba, ya lissafo karin wasu ‘yan siyasar da suka bi ta kan wannan doka, wadanda suka hada da Gwamna Ben Ayade na Jihar Kuros Ribas, Tambuwal tare da Bala Mohammed na Jihar Bauchi.

Lawan
Muhammad Maitela
+ postsBio
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Kashe Kansila A Adamawa

'Yan Bindiga Sun Kashe Kansila A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.