• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Sanda Sun Kashe Dan Bindiga, Sun Kwato AK-47 A Zamfara

by Sadiq
3 years ago
in Labarai
0
‘Yan Sanda Sun Kashe Dan Bindiga, Sun Kwato AK-47 A Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’an ‘yan sanda a Jihar Zamfara sun kashe wani dan bindiga tare da kwato bindiga kirar AK 47 da alburusai 18 a wani artabu da suka yi a kauyukan Saran Gamawa da Anguwar Mata da ke Karamar Hukumar Gummi a Jihar.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin  rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara, SP Muhammad Shehu, ya fitar a Gusau ranar a Litinin.

  • Za A Shafe Shekaru Kafin A Kawo Karshen Yakin Ukraine Da Rasha —NATO
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Coci, Sun Kashe Mutane 3 A Kaduna

“A ranar 19 ga Yuni, 2022, jami’an ‘yan sandan da aka tura ta hanyar Gummi/Bukkuyum, sun samu kiran gaggawa cewa, ‘yan ta’adda dauke da makamai a kan babura sun kai farmaki Saran Gamawa da kauyukan Unguwar Mata da ke makwabtaka da su da nufin sace mutanen da ba su ji ba ba su gani ba.

“Rundunar ‘yan sanda tare da hadin gwiwar ‘yan banga na kauyukan da lamarin ya shafa, sun hada karfi da karfe tare wajen yakar ‘yan ta’addan a wani kazamin artabu da aka dauki tsawon sa’o’i ana yi.

“Sakamakon haka, daya daga cikin ‘yan ta’addan ya samu munanan raunuka, an samu bindiga kirar Ak 47 a wajen dan bindigar, yayin da wasu da dama suka tsere cikin dajin da raunukan harbin bindiga daban-daban,” in ji Shehu.

Labarai Masu Nasaba

Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Ayuba Elkanah, ya yaba da jajircewar da ‘yan sandan suka yi, ya kuma bukace su da kada su yi kasa a gwiwa wajen ganin rundunar ta kare rayuka da dukiyoyin mutanen da ba su ji ba ba su gani ba a jihar.

Elkanah ya kuma umarci Kwamandan yankin Anka da DPO da ke makwabtaka da su tura tawagar hadin gwiwa don ci gaba da sintiri don dakile ci gaba da kai hare-hare a kan al’ummomin da ke yankunan.

Ya ce rundunar ta kuma tura domin ceto mutanen biyu da maharan suka yi garkuwa da su kafin isowar ‘yan sanda.

“Yayin da yake tabbatar da kudurin rundunar na kare rayuka da dukiyoyi a jihar, ya yi kira ga jama’a da su ba ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro hadin kai a kokarin kawar da ‘yan bindiga a jihar,” in ji kakakin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan SandaArtabuDan BindigaYan bindigaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Za A Shafe Shekaru Kafin A Kawo Karshen Yakin Ukraine Da Rasha —NATO

Next Post

Ganduje Ya Nada Baffa A Matsayin Shugaban Hukumar Kare Hakkin Masu Siye Da Siyarwa 

Related

‘Yan Bindiga Sun Sake Kashe Mutum 6 A Ƙauyukan Filato, Sun Jikkata Wasu
Labarai

Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato

47 minutes ago
An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa
Labarai

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

9 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

10 hours ago
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma
Labarai

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

11 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

12 hours ago
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano
Manyan Labarai

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

13 hours ago
Next Post
Ganduje Ya Nada Baffa A Matsayin Shugaban Hukumar Kare Hakkin Masu Siye Da Siyarwa 

Ganduje Ya Nada Baffa A Matsayin Shugaban Hukumar Kare Hakkin Masu Siye Da Siyarwa 

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sake Kashe Mutum 6 A Ƙauyukan Filato, Sun Jikkata Wasu

Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato

July 2, 2025
An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.