Rundunar ‘yansanda Jihar Legas ta ceto wani yaro mai suna Emmanuel Adeleke daga hannun wanda ya sace shi.
Kakakin rundunar ‘yansandan, SP Benjamin Hundeyin, ne ya bayyana hakan a ranar Laraba a shafinsa na Twitter da kamfanin dillancin labarai (NAN) ya sanyawa hannu.
- Dakarun Soji A Jihar Kaduna Sun Kara Kashe Wani Jagoran ‘Yan Bindiga Gudau Kachalla
- Ganduje Ya Karrama Dan Sandan Da Ya Ki Karbar Cin Hancin Dala $200,000 A Kano
Ya ce yaron mai shekaru tsakanin 11zuwa 14, ya kubuta, don haka aka kai shi asibiti inda yake jinya a can.
“Abin da zamu iya cewa, an sace shi ne a Jakande, unguwar Ikotun a Legas a ranar Lahadi, 13 ga watan Nuwamba, 2022. Ya ba da sunansa a matsayin Emmanuel Timilehin Adeleke.
“Ya ba da sunayen iyayensa da adireshi daban-daban. Yana da shekaru tsakanin 11 zuwa 14.”
Hundeyin ya bukaci duk jama’a da su bayar da bayanai da za su taimaka inda za a gano iyayen yaron suke.
“Duk wani bayani da zai taimaka wajen gano iyayensa ko masu kula da shi zai taimaka,” in ji kakakin rundunar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp