• English
  • Business News
Saturday, October 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Kama Kasurguman ‘Yan Bindiga 2, Sun Ceto Mutane 7, Sun Kwato 2.1m Kudin Fansa

by Sadiq
3 years ago
'Yansanda

Rundunar ‘yansandan Jihar Neja ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da yin garkuwa da mutane a karamar hukumar Gurara a jihar a ranar Juma’a.

Rundunar a cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP W. A. ​​Abiodun, ya sanya wa hannu a ranar Asabar, ta ce tun a ranar Juma’a, 27 ga watan Janairu, 2023 da misalin karfe 10:30 na safe, bisa ga bayanan da aka samu cewa an ga wasu mutane da ake zargin ‘yan bindiga ne.

  • Son Rai Da Rashin Cancantar Jarumai Ke Gurbata Al’adu A Fina-finanmu –Daushe
  • ’Yar Kasuwa Elizabeth Homes: Labarin Tashe Da Rushewarta (II)

DPO na reshen Lambata da ke karamar hukumar Gurara, ya tara tawagar ‘yansanda tare da ’yan banga zuwa yankin, inda suka cafke mutane biyun da ake zargin.

“Lokacin da ake yi musu tambayoyi, sun amsa cewa suna cikin kungiyar masu garkuwa da mutane suka addabi yankin Gwagwalada a Abuja, Lambata da Kafin-Koro.

“An kwato wayoyin hannu guda uku daga hannun wadanda ake zargin, sannan kuma an samu kudi miliyan biyu da na5ira dubu dari da suka karba a matsayin kudin fansa domin a sako mutanen biyu da suka sace a Gwagwalada.

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari

Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

“Sun kuma kara da cewa sun ajiye wadanda suka yi garkuwa da su a dajin Gwalo.

“An ceto wadanda lamarin ya rutsa da su ba tare da sun samu rauni ba, an kai su cibiyar lafiya ta FCM domin kula da lafiyarsu, sannan an mika su ga iyalansu,” in ji kakakin.

Ya kara da cewa kwamishinan ‘yansandan jihar, CP Ogundele J. Ayodeji, ya tabbatar wa jama’a cewar rundunar za ta ci gaba da gudanar da ayyukanta don tabbatar da tsaro a jihar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari

October 11, 2025
Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
Manyan Labarai

Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

October 11, 2025
Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Next Post
Babu Wata Baraka Tsakanina Da Buhari – Tinubu

Babu Wata Baraka Tsakanina Da Buhari - Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa

Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa

October 11, 2025
Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari

Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari

October 11, 2025
Wakiliyar CMG Ta Zanta Da Farfesa Jeffrey Sachs Na Jami’ar Columbia

Wakiliyar CMG Ta Zanta Da Farfesa Jeffrey Sachs Na Jami’ar Columbia

October 11, 2025
Li Qiang Ya Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Koriya Ta Arewa

Li Qiang Ya Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Koriya Ta Arewa

October 11, 2025
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

October 11, 2025
Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi

Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi

October 11, 2025
Gwamna Aliyu Ya Tsige Hakimai 15 Na Sokoto

A Ba Mu Makamai Don Kare Kanmu – Jama’ar Sakkwato

October 11, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 9, Sun Ƙwato Naira Miliyan 5 A Borno

Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 9, Sun Ƙwato Naira Miliyan 5 A Borno

October 11, 2025
Ta’addanci

Sojoji Sun Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Lalata Kayayyakin Gwamnati A Binuwe

October 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.