ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Son Rai Da Rashin Cancantar Jarumai Ke Gurbata Al’adu A Fina-finanmu –Daushe

by Rabi'at Sidi Bala
3 years ago
Daushe

Fitaccen Jarumin da ya shahara ya kuma dade a fannin fina-finan barkwanci da ya shafe shekara 28 cikin masana’antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood, RABI’U IBRAHIM wanda aka fi sani da DAUSHE, ya tattauna da wakiliyarmu RABI’AT SIDI BALA, inda ya bayyana wa masu karatu matsaloli da kalubalen da ya fuskanta a masana’antar, tare da yin kira ga gwamnati a kan abubuwan da suka kamata a yi domin ci gaban masana’antar Kannywood, har ma da wasu batutuwan da suka shafi rayuwarsa. Ga dai yadda tattaunawar ta gudana:

Da farko za ka fadawa masu karatu cikakken sunanka tare da sunan da aka fi saninka da shi…

Sunana Rabi’u Ibrahim (Daushe).

ADVERTISEMENT

Ko za ka fada wa masu karatu dan takaitaccen tarihinka?

To Ni dai Rabiu ibrahim (Daushe), an haife ni a karamar hukumar Ajingi cikin Jihar kano, shekara ta 1979 watan Yuni. Na yi makarantar firamare a nan garin Ajingi, wanda daga baya mahaifina ya sami canjin aikin zuwa garin Wudil, cikin Jihar Kano. Nan na ci gaba da firamare da kuma Sakandare, wato makarantar horan malamai ta garin Wudil  ‘T.C Collage Wudil’. Inda na shiga harkokin kasuwanci daga baya.

LABARAI MASU NASABA

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

Ya Kamata Mawaƙa Su Guji Munafunci Da Hassada Su Rungumi Juna —Fati UK

Ta yaya ka samo sunan Daushe?

Na samo sunan daushe ne a wani gari da ake kira da misau cikin Jihar Bauchi a lokacin da nake koyan Dirama, muna yawo ne da wasu mutane kafin mu hadu da Alh. Rabilu Musa (Dan ibro) a wannan tafiyar da muka yi tafiya ce ta kwatar kai ba ni da sunan da nake amfani da shi a wasa ko a dirama saboda haka sai Jagoran tafiyar ya ce kowa sai ya samo sunan da za a rinka kiransa da shi a fagen dirama, ta nan ne na kirkiro wa kaina suna da Daushe, kin ji ta inda na samo wa kaina sunan Daushe.

Me ya ja hankalinka har ka tsunduma harkar fim?

Ganin kullum hausawa na watsi da Al’adarsu  suna aro wadda ba tasu ba, da kuma sanbada gudummawa wajan tallata kalmar malan bahaushe da tuna masa Al’adunsa da Abincinsa da kuma sake jawo shi nuna masa harshensa na da tasiri a duniya baki daya.

Wacce irin rawa kake takawa a masana’antar Kannywood?

Ina taka rawa mafi mataki na daya shi ne; matsayin uba ko magidanci, ko maigari, ko Alkali, ko sarki, ko dan sanda ko soja ko likita da dai sauran gurare mafi girma a cikin fina-finan Hausa.

Kamar fannin ba da umarni ko shiryawa ko rubutawa ko makamancin haka fa?

Ina rubutun labari da kaina kuma ina ba da umarni, nan take na sha zuwa aiki a matsayin Jarumi sai mai aikin ya ce ni zan ci gaba da ba da umarni, na yi haka ba sau daya ba, ba sau biyu ba. Kuma ina ‘Producing’ da kaina, na sayar ko kuma na ba da kudi a yi min ba tare da an san nawa ne ba.

Ya kake kallon yadda fim ke gudana a yanzu, musamman da ka yi magana a kan al’ada, da yawan mutane na kallon fim din Hausa ba a yin sa bisa al’ada, sai ma wasu al’adun da ake arowa a ko da yaushe, me za ka ce a kan hakan?

Hakan yana da nasaba da barin Al’adunmu da muka yi a baya, da kuma dimaucewar mutanen cikin masana’antar da suka yi da yin aikin son kai ko son rai na rashin duba cancantar Jarumi ko Jaruma, wajan sanya su a gurbin da ya dace.To sun hada kansu da aiki a yanzu dai sakamakon rikon sakainar kashi da akai wa sabgar.

Ya gwagwarmayar shiga masana’antar ta kasance a wancen lokacin?

Aike na kawai ake yi tsahon shekara 7 ina fama da aike da sayan sigari, da siyo wa mata abinci da yi musu wanki, haka nai ta fama.

Lokacin da ka fara tunanin shiga harkar fim, bayan ka sanar da iyayenka, ko akwai wani kalubale da ka fuskanta daga gare su?

Na fuskanta, amma daga baya na ce kawai su yi min Addu’a idan ba alkairi Allah ya canza min kawai.

Za ka ka yi shekara nawa da fara fim?

Zan yi shekara 28, zuwa da tara.

A wanne fim ka fara fitowa kuma wacce rawa ka taka cikin fim din?

Almajirai, na fito a magidanci wanda Almajiran suke shigowa gidana su dauke min Abinci nake fitowa ina ihu ina cewa Ihu  taliyata ‘yar Gwabnati.

Ko za ka iya tuna yawan adadin fina-finan da ka fito ciki?

Ba zan iya ba wallahi Allah, saboda jiya ba yau ba ce, a kalla za su kai dubu goma.

Ya farkon farawarka ya kasance, musamman yadda kake sabo a lokacin?

Na sha fama da kalubale kamar tsangwama da kyara da hantara da wuni da yunwa da kuma  rashin sakar min fuska a gun wadanda na samu a ciki lokacin da na zo na samu abokan aiki.

Me ya sa ka zabi zama a bangaren Camama dan taka rawa ciki?

Saboda shi ne fim din da sako ya fi tafiya ga dan kallo nan take kuma cikin nishadi za ka kalla duk ai da ‘ya’yanka ba tare da jin kunya ba.

Ya za ka bambanta wa masu karatu bambancin fina-finan baya dana yanzu musamman idan ka cire bangaren ‘yan camama da kuke yi ka hada su waje guda?

Bambanci a bayyane yake ai idan kika dubi sa tufafi za ki ga na da, hatta kayan da samari maza ke sakawa hannun rigar har yawa yake yi, saboda tafiya a kan  tsarin Addini da Al’ada.

Akwai wata murya da kake yi cikin fina-finanka wanda kuma a zahiri gashi dai ba haka muryarka take ba, shin koya maka aka yi lokacin da ka fara fim ko kuwa kai da kanka ka kirkiri abarka dan kara armashin shirin?

Ba wanda ya koya min maida hankali da san na birge mai kallona nai ta sarrafa ta har tazama haka a yau.

Akwai wata riga da kake yawan sakawa a cikin mafi yawan fina-finanka, shin rigarka ce kai ka ware ta dan shirin fim kawai, ko kuwa a bangaren aikinku ne na ‘yan camama ake rabawa kowa rigarsa, ta yadda duk shirin da zai yi sai ya dauko ya saka hade da hula ko kuwa?

Kowa ke siyan kayansa ni nake dinka kayata da hular dan dacewa da salona.

Daushe
Rabi'at Sidi Bala
+ postsBio
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Yadda Al’umma Suka Gudanar Da Bukukuwan Sallah Duk Da Matsin Tattalin Arziki
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    GORON JUMA’A 29-05-2027
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Yadda Za Ku Tattala Kuɗaɗen Da Ke Shigowa Hannu Domin Ci Gaban Rayuwa

MASU ALAKA

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro
Nishadi

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Nishadi

Ya Kamata Mawaƙa Su Guji Munafunci Da Hassada Su Rungumi Juna —Fati UK

May 23, 2026
Har Yanzu Burina Bai Cika Ba A Waka —Hadiza Maikano
Nishadi

Har Yanzu Burina Bai Cika Ba A Waka —Hadiza Maikano

May 16, 2026
Next Post
‘Yansanda Sun Kama Kasurguman ‘Yan Bindiga 2, Sun Ceto Mutane 7, Sun Kwato 2.1m Kudin Fansa

'Yansanda Sun Kama Kasurguman 'Yan Bindiga 2, Sun Ceto Mutane 7, Sun Kwato 2.1m Kudin Fansa

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.