• English
  • Business News
Friday, September 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

by Sadiq
2 hours ago
in Manyan Labarai
0
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ’Yansandan Jihar Jigawa ta kama mutane biyu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne tare da wasu mutane 156 bisa laifuka daban-daban cikin watanni biyu da suka gabata.

Kwamishinan ’Yansandan jihar, CP Dahiru Muhammad ne, ya shaida wa manema labarai cewa ɗaya daga cikin waɗanda aka kama, Adamu Musa mai shekara 47 daga unguwar Yalwawa a Dutse, shugaban masu garkuwa da mutane ne.

  • Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
  • Sojoji Sun Kama Ɗan Bindiga Ɗauke Da Makamai A Jihar Filato

Ana zargin ya yi garkuwa da mutane huɗu daga ƙaramar hukumar Sumaila ta Jihar Kano, inda ya tsare su a ƙauyen Baranda na ƙaramar  hukumar Dutse.

Ya saki mutanen ne bayan ya karɓi kuɗin fansa har Naira miliyan takwas da babur ɗaya wanda darajarsa ta kai Naira miliyan ɗaya.

Haka kuma, a ranar 29 ga watan Agusta, 2025, da misalin ƙarfe 3 na rana, ’yansanda tare da jami’an sa-kai sun kama wani da ake zargi da garkuwa da mutane da fashi makami ne.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kama Ɗan Bindiga Ɗauke Da Makamai A Jihar Filato

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Wanda aka kama sunansa iro Garba mai shekaru 25 daga Zangwaye Fulani a ƙaramar hukumar Ajingi a Jihar Kano.

Ya amsa cewa shi da wasu mutane huɗu sun yi garkuwa da mutane a Kano, Jigawa da Bauchi.

An kuma samu rigunan sojoji guda uku a hannunsa.

Kwamishinan ya ce ana ci gaba da ƙoƙarin kama sauran mutane huɗun da ake zargi da hannu a garkuwar da ta faru a Sumaila, da ke Jihar Kano.

A wani lamari kuma, ’yansanda sun kama mutane huɗu da ake zargi da fasa shago a ƙaramar hukumar Malam Madori.

Waɗanda aka kama sun haɗa da: Nuhu Yusif Saleh (19), Hassan Ibrahim (19), da Nura Musa (22).

An ƙwato akwati mai ɗauke da kuɗi Naira 870,000, abun cajin waya guda biyu, na’urar PoS, wayoyi guda 20, da lasifiƙa daga hannunsu.

Jimillar mutanen da aka kama a cikin watanni biyu sun kai 156 bisa laifuka daban-daban, ciki har da safarar makamai, fashi da makami, kisan kai, fyaɗe, lalata kayan gwamnati, fataucin miyagun ƙwayoyi da sata.

Kayan da aka ƙwato sun haɗa da bindiga AK-47 guda biyu, motoci guda uku, adaidaita sahu guda ɗaya, wayoyi guda 23, shanun sata guda 14, da kuma miyagun ƙwayoyi kamar tramadol, diazepam, exol, tabar wiwi, da sauransu.

CP Muhammad ya tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da yaƙi da laifuka da kuma safarar miyagun ƙwayoyi a faɗin Jihar Jigawa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaGarkuwaJigawa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

Next Post

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

Related

Sojoji Sun Kwato Makamai Da Babura, Sun Ceto Mutane 3 A Kaduna 
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Bindiga Ɗauke Da Makamai A Jihar Filato

5 hours ago
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

13 hours ago
Ministan Tsaro
Manyan Labarai

Dawowar Matsalar Tsaro: Ta Haifar Da Cece-kuce Kan Daukar Matakin Kare Kai

14 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

23 hours ago
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Fara Hutun Aiki Na Kwanaki 10 A Faransa Da Birtaniya

1 day ago
Ibtila’in Ambaliyar Ruwa: Halin Da Birnin Maiduguri Ya Tsinci Kansa A Ciki
Manyan Labarai

Gargaɗi: Ƙauyuka 43 A Jihohi 14 Na Fuskantar Barazanar Ambaliyar Ruwa 

1 day ago
Next Post
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

LABARAI MASU NASABA

Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 5, 2025
Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

September 5, 2025
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

September 5, 2025
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

September 5, 2025
Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

September 5, 2025
Muddin Nahiyar Afirka Ta Farka Ba Za A Iya Raina Ta Ba

Yara 400,000 Ne Ke Kamuwa Da Cutar Kansa Duk Shekara A Duniya

September 5, 2025
Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

September 5, 2025
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Kwalaben Akuskura Sama Da 8,000 A Kano

September 5, 2025
'Yan Bindiga

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

September 5, 2025
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.