• English
  • Business News
Thursday, June 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Kama Matasa 51 da Ake Zargi Da Faɗan Daba A Kano

by Sadiq
2 days ago
in Manyan Labarai
0
‘Yansanda Sun Kama Matasa 51 da Ake Zargi Da Faɗan Daba A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansandan Jihar Kano, ta kama matasa 51 da ake zargi da addabar jihar da faɗan daba. 

Haka kuma ta ƙwato makamai masu hatsari da miyagun ƙwayoyi a yayin wani samame da ta kai na tsawon kwana uku a sassa daban-daban na birnin Kano.

  • Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu
  • Sarkin Musulmi Ya Nuna Baƙin Ciki Kan Kisan Kiyashi A Binuwe

An gudanar da samamen ne daga ranar Juma’a, 13 ga watan Yuni, zuwa Lahadi, 15 ga watan Yuni.

‘Yansanda sun mayar da hankali wuraren da aka fi samun aikata laifi a ƙananan hukumomin Birni, Dala, Gwale, da Tarauni.

Sauran sun haɗa da unguwannin Kofar Mata, Zage, Kurna, Rijiyar Lemo, Dorayi, Hotoro da Sheka.

Labarai Masu Nasaba

Lakurawa Sun Sanya Dokar Hana Sayar Da Shanu A Kebbi

An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina

DSP Hussaini Abdullahi, Mataimakin Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a madadin Kwamishinan ‘Yansandan Jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, a ranar Litinin, 16 ga watan Yuni.

Yawancin waɗanda aka kama matasa ne ‘yan tsakanin shekaru 15 zuwa 39.

Ana zargin su da shiga harkar daba, faɗa a titi da kuma amfani da miyagun ƙwayoyi.

‘Yansanda sun ce wannan samame wani ɓangare ne na ƙoƙarin da suke yi na daƙile daba da dawo da zaman lafiya a birnin Kano.

Kwamishinan ‘Yansandan ya ja kunnen jama’a ka da su riƙa ɗaukar makamai a yayin shagulgulan gargajiya kamar “Gangi”, ko kuma nuna makamai a shafukan sada zumunta kamar TikTok, Facebook, Instagram da X, domin hakan na jawo wa matasa sha’awar shiga ayyukan daba.

Sanarwar ta kuma yi gargaɗi ga iyaye, da kuma masu ƙera makamai cewa duk wanda aka samu yana ɓoye ko taimaka wa ‘yan daba, ko kuma yana ƙera makaman da ake amfani da su wajen tashin hankali, za a gudanar da bincike a kansa tare da gurfanar da shi a gaban kotu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaFaɗan DabakanoMatasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu

Next Post

Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga

Related

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama
Manyan Labarai

Lakurawa Sun Sanya Dokar Hana Sayar Da Shanu A Kebbi

6 minutes ago
Kawayen amarya
Manyan Labarai

An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina

9 hours ago
EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana
Manyan Labarai

EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana

13 hours ago
Tinubu Ya Kai Ziyara Benuwe Sakamakon Kisan Kiyashi Da Aka Yi Wa Jama’a
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kai Ziyara Benuwe Sakamakon Kisan Kiyashi Da Aka Yi Wa Jama’a

17 hours ago
PDP Ta Yi Satar Amsa Daga Manufofin Buhari – Tinubu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Kwaso ‘Yan Nijeriya Da Suka Maƙale A Isra’ila Da Iran

20 hours ago
An Ɗaure Wani Mutum Wata 6 Kan Satar Takalma A Masallaci A Kaduna
Manyan Labarai

An Ɗaure Wani Mutum Wata 6 Kan Satar Takalma A Masallaci A Kaduna

21 hours ago
Next Post
Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga

Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun 'Yan Bindiga

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama

Lakurawa Sun Sanya Dokar Hana Sayar Da Shanu A Kebbi

June 19, 2025
Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

June 18, 2025
Kawayen amarya

An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina

June 18, 2025
Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

June 18, 2025
WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

June 18, 2025
Dan Wasan Gaban Chelsea, Murdyk Ka Iya Shafe Shekaru 4 Ba Tare Da Ya Buga Wasa Ba

Dan Wasan Gaban Chelsea, Murdyk Ka Iya Shafe Shekaru 4 Ba Tare Da Ya Buga Wasa Ba

June 18, 2025
Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

June 18, 2025
Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital

Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital

June 18, 2025
Mutane Hudu Sun Mutu, An Ceto Wasu A Hatsarin Kwalekwale A Yauri

Mutane Hudu Sun Mutu, An Ceto Wasu A Hatsarin Kwalekwale A Yauri

June 18, 2025
“Ruhin Sin Da Tsakiyar Asiya” Ya Jagoranci Bude Wani Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Yanki

“Ruhin Sin Da Tsakiyar Asiya” Ya Jagoranci Bude Wani Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Yanki

June 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.