• English
  • Business News
Tuesday, June 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Kama Mutane 88 Kan Aikata Laifuka A Katsina

by Sadiq
1 year ago
in Labarai
0
‘Yansanda Sun Kama Mutane 88 Kan Aikata Laifuka A Katsina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansandan Jihar Katsina, ta kama wasu mutane 88 da ake zargi da aikata manyan laifuka guda 59 a jihar a cikin watan Fabrairu.

Kakakin rundunar ‘yansandan, ASP Abubakar Sadiq-Aliyu, ya bayyana haka a Katsina ranar Laraba.

  • NiMet Ta Yi Hasashen Bullar Zazzabin Cizon Sauro A Watan Maris Da Afrilu
  • Jakadun Kasa Da Kasa Dake Sin: Kuzarin Tattalin Arzikin Sin Zai Amfani Kasashen Duniya

A cewarsa, an kama wadanda ake zargin ne bisa zarginsu da hannu a fashi da makami, garkuwa da mutane, satar shanu, da kuma kisan gilla da dai sauransu.

Ya ce ‘yansanda sun shigar da kararraki 49 a gaban kotuna kan wasu da aka kama.

Sadiq-Aliyu ya bayyana cewa an kama mutane 13 da ake zargi da aikata fashi da makami, 12 da laifin kisan kai, 19 da laifin fyade, uku da laifin yin garkuwa, yayin da sauran kuma aka kama su kan wasu laifuka.

Labarai Masu Nasaba

Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

Ya ci gaba da cewa, an kama mutanen uku da ake zargin masu garkuwa da mutane ne a wani samame na hadin gwiwa da rundunar ‘yansandan Katsina da babban birnin tarayya suka yi.

Kakakin rundunar ‘yansandan ya bayyana sunayensu da Hassan Ibrahim mai shekaru 25 da Ibrahim Ishaq mai shekaru 33 da Shafi’u Zubairu mai shekaru 30 duk a kauyen Kakabawa da ke Karamar Hukumar Kurfi ta jihar.

A cewarsa, yayin da ake yi musu tambayoyi, wadanda ake zargin sun amsa laifin aikata ta’addanci a kananan hukumomin Kurfi da Safana.

Ya kara da cewa wadanda ake zargin sun ambaci wasu miyagun ‘yan bindiga guda uku da suke aiki da su, wadanda a yanzu suke hannun hukuma a jihar.

Sadiq-Aliyu ya kara da cewa an kama wani Bilyaminu Muhammad mai shekaru 32 a kauyen Zago da ke karamar hukumar Arewa ta Kebbi bisa laifin mallakar harsashi guda bakwai ba bisa ka’ida ba.

A cewarsa, an ceto mutane 72 da aka yi garkuwa da su a fadin jihar a cikin watan Fabrairu tare da kwato dabbobi 500 da aka sace.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaKatsina
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Kashe Dan Bindiga, Sun Ceto Mutane 15 A Zamfara

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe Makiyayi Da Shanu 35 A Wani Sabon Harin A Filato

Related

Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027
Labarai

Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

2 hours ago
Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta
Labarai

Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

3 hours ago
Sabbin Ministoci
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6

5 hours ago
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba
Ra'ayi Riga

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

5 hours ago
Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC
Manyan Labarai

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

8 hours ago
An Cafke Mutum 22 Kan Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato – Uba Sani
Manyan Labarai

An Cafke Mutum 22 Kan Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato – Uba Sani

12 hours ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Kashe Makiyayi Da Shanu 35 A Wani Sabon Harin A Filato

‘Yan Bindiga Sun Kashe Makiyayi Da Shanu 35 A Wani Sabon Harin A Filato

LABARAI MASU NASABA

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

June 24, 2025
Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

June 24, 2025
Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

June 24, 2025
Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

June 24, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6

June 24, 2025
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

June 24, 2025
Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

June 24, 2025
Sabuwar Shugabar Kwamitin Wasannin Olympics Na Duniya Na Fatan Sake Ziyartar Kasar Sin

Sabuwar Shugabar Kwamitin Wasannin Olympics Na Duniya Na Fatan Sake Ziyartar Kasar Sin

June 24, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Bikin Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan Da Yakin Kin Tafarkin Murdiya

Xi Jinping Zai Halarci Bikin Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan Da Yakin Kin Tafarkin Murdiya

June 24, 2025
Shugaban CMG Ya Zanta Da Manyan Jami’an IOC

Shugaban CMG Ya Zanta Da Manyan Jami’an IOC

June 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.