ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NiMet Ta Yi Hasashen Bullar Zazzabin Cizon Sauro A Watan Maris Da Afrilu

by Salim Sani Shehu
2 years ago
NiMet

Hukumar kula da yanayi ta kasa (NiMet), ta yi hasashe tare da nuna damuwa kan yanayin da za a shiga nan gaba a yanayi zafi.

Sauyin yanayi wanda ya hada da zafi, sanyi da kuma samun ruwan sama suna tasiri sosai ga barkewar cututtuka.

  • An Kama ‘Yan Sintiri 10 Kan Zargin Kashe Limamin Garin Mada
  • Boko Haram Ta Kone Gidajen Da Aka Gina Wa ’Yan Gudun Hijira A Borno

Cututtukan sun hada zazzabin cizon sauro, sankarau da kuma wasu cuttutuka da suke da alaka da yanayin sauyin yanayin.

ADVERTISEMENT

Cibiyar Bincike ta Duniya da Yanayi ta Al’umma (IRI), ta bayyana cewa yanayi zafi zai kai kashi 80 da kuma matsakaicin zafin jiki zuwa kashi 18 da 32 da yanayin zafi sama da sama da kashi 60 su suke taimakawa wajen kyankyashe kwayoyin halittar cutar.

Hukumar ta ce a watan Janairun 2024 yanayin zai iya bai wa kwayoyin halittar sauro damar zuba kwayayensa da kuma samun damar kyankyashe su, wanda hakan ne ke taimakawa wajen yada cutar.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa

Hukumar ta ce irin wannan yanayin shi ne ake tunani da kuma hasashen cewa zai faru a wasu daga cikin yankunan Nijeriya.

Hukumar ta jaddada cewa sauyin yanayi da ake samu wanda yake sauyawa ba tare da daukar lokaci ba.

Don haka, da zarar wadannan yanayi sun daidaita, akwai yiwuwar kamuwa da cutar zazzabin cizon sauro.

Ana sa ran zuwa watan Afrilu, hukumar ta yi hasashen yiwuwar kamuwa da cutar zazzabin cizon sauro a jihohin kudancin kasar nan, wanda ya bambanta da kananan da ma wasu yankuna.

Haka zalika, hukumar ta yi hasashen irin wannan yanayin a watan Maris, inda ta ce akwai yiwuwar cutar zazzabin cizon sauro a jihohin Sakkwato da Katsina da Zamfara da kuma Jihar Kano.

Sauran jihohin sun hada da Jigawa da Bauchi da Yobe da Borno.

Sannan hukumar ta kuma bayar da shawara ga yankunan Kebbi da Neja da Zamfara da Kaduna da Taraba da Adamawa da Filato da Benuwe da Kwara da Kogi da Nasarawa da kuma babban birnin tarayya Abuja, su kanasance cikin shiri.

NiMet
Salim Sani Shehu
+ postsBio
  • Salim Sani Shehu
    https://hausa.leadership.ng/author/salim-sani-shehu/
    Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda, Sun Ƙwato Makamai Da Abubuwan Fashewa
  • Salim Sani Shehu
    https://hausa.leadership.ng/author/salim-sani-shehu/
    Gwamnatin Jigawa Ta Bayar Da Umarnin Bincikar Tsohon Gwamnan Jihar Badaru
  • Salim Sani Shehu
    https://hausa.leadership.ng/author/salim-sani-shehu/
    An Sake Samun Ɓullar Cutar Korona A Nijeriya
  • Salim Sani Shehu
    https://hausa.leadership.ng/author/salim-sani-shehu/
    Ƙarin Farashin Man Fetur: TUC Ta Shawarci Gwamnati Ta Tallafawa Matatun Mai Na Cikin Gida

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa
Manyan Labarai

Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa

June 26, 2026
An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai
Rahotonni

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

June 26, 2026
Next Post
Za Mu Kwace Lasisin Kamfanonin Wutar Lantarkin Nijeriya – Minista

Za Mu Kwace Lasisin Kamfanonin Wutar Lantarkin Nijeriya - Minista

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

June 26, 2026
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
sikila

Buƙatar Mayar Da Hankali Wajen Kawo Ƙarshen Ciwon Sikila A Nijeriya

June 26, 2026
Sin Ta Bankado Laifukan Miyagun Kwayoyi 12,000 A Watanni Biyar Na Farkon Bana

Sin Ta Bankado Laifukan Miyagun Kwayoyi 12,000 A Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 26, 2026
makarfi

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

June 26, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa

Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa

June 26, 2026
An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

June 26, 2026
Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila

Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila

June 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.