• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansandan Sun Cafke Mutane 5 Kan Zargin Yin Garkuwa Da Mutane, Sun Kwato Miliyan 4 

by Sadiq
3 years ago
in Labarai
0
‘Yansandan Sun Cafke Mutane 5 Kan Zargin Yin Garkuwa Da Mutane, Sun Kwato Miliyan 4 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansandan Jihar Adamawa, ta ce jami’anta sun kama wasu mutane biyar da ake zargin masu garkuwa da mutane ne. 

Ta kuma kara da cewa jami’an sun kwato kudi Naira miliyan 4,079,000 daga hannun wadanda ake zargin.

  • ‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2, Sun Kwato Makamai 
  • Gwamnatin Kogi Ta Bai Wa Dangote Sa’o’i 48 Ya Kulle kamfanin Simintinsa Da Ke Obajana

Hakan na kunshe ne a wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yansandan jihar Adamawa, SP Suleiman Yahaya Nguroje, ya fitar ranar Juma’a.

A cewar sanarwar, jami’an rundunar, a ranar 9/10/2022, sun katse wata hanyar sadarwa da ke da alaka da kungiyoyin ta’addanci guda biyar a kananan hukumomin Mubi ta Arewa da Kudu.

Rundunar ta ce jami’an sun samu rahoton yin garkuwa da wani matashi mai suna Mustapha Aliyu Fadil dan shekara 8 a garin Mubi tare da kai shi otal din Barassa da ke Maraba Mubi.

Labarai Masu Nasaba

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

Ya ce nan take rundunar ta tattara jami’anta da ke da alaka da Hukumar Leken Asiri ta Jihar (SIB) suka gudanar da aikin, an kuma yi nasara.

A cewarsa, an samu nasarar kwato makudan kudi har miliyan hudu da da dubu saba’in da tara daga cikin Naira miliyan biyar, da aka biya a matsayin kudin fansa.

Ya ce wadanda ake zargin sun hada baki ne suka tafi da wanda suka sace inda suka tsare shi har na tsawon kwanaki biyu har sai an biya su kudin fansa miliyan biyar kamar yadda suka nema kafin a sako wanda abun ya shafa.

A cewarsa, kwamishinan ‘yansandan, SK Akande, yayin da yake yabawa jami’an bisa yadda suka katse hanyoyin sadarwa ta hanyar nuna kwarewa, ya umarci jami’an da su ci gaba da gudanar da irin wannan aikin, a matsayin dabarun binciken laifuka da masu aikata laifuka a cikin jihar da kewaye.

“CP ya yi kira ga jama’a da su sanar da ‘yansanda a ko da yaushe game da inda masu laifi suke da maboyarsu, musamman ma wadanda ke da ake da kokwanto a kan su,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaAdamawaGarkuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yajin Aikin ASUU: Muna Neman Afuwar Dalibai Da Iyaye – Gwamnatin Tarayya

Next Post

Mbappe Ne Ya Fi Kowanne Dan Wasa Daraja

Related

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

4 hours ago
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

5 hours ago
Ganduje Ba Zai Hana Kwankwaso Shiga APC Ba
Labarai

Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki

6 hours ago
Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

9 hours ago
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

18 hours ago
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu
Labarai

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

20 hours ago
Next Post
Mbappe Ne Ya Fi Kowanne Dan Wasa Daraja

Mbappe Ne Ya Fi Kowanne Dan Wasa Daraja

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

June 30, 2025
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

June 30, 2025
Sin Ta Kalubalanci Kasashen Yammacin Duniya Da Su Tuna Da Laifinsu Na Mulkin Mallaka

Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba

June 30, 2025
Ganduje Ba Zai Hana Kwankwaso Shiga APC Ba

Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki

June 30, 2025
Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

June 30, 2025
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.