ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansandan Sun Cafke Mutane 5 Kan Zargin Yin Garkuwa Da Mutane, Sun Kwato Miliyan 4 

by Sadiq
4 years ago
'Yansanda

Rundunar ‘yansandan Jihar Adamawa, ta ce jami’anta sun kama wasu mutane biyar da ake zargin masu garkuwa da mutane ne. 

Ta kuma kara da cewa jami’an sun kwato kudi Naira miliyan 4,079,000 daga hannun wadanda ake zargin.

  • ‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2, Sun Kwato Makamai 
  • Gwamnatin Kogi Ta Bai Wa Dangote Sa’o’i 48 Ya Kulle kamfanin Simintinsa Da Ke Obajana

Hakan na kunshe ne a wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yansandan jihar Adamawa, SP Suleiman Yahaya Nguroje, ya fitar ranar Juma’a.

ADVERTISEMENT

A cewar sanarwar, jami’an rundunar, a ranar 9/10/2022, sun katse wata hanyar sadarwa da ke da alaka da kungiyoyin ta’addanci guda biyar a kananan hukumomin Mubi ta Arewa da Kudu.

Rundunar ta ce jami’an sun samu rahoton yin garkuwa da wani matashi mai suna Mustapha Aliyu Fadil dan shekara 8 a garin Mubi tare da kai shi otal din Barassa da ke Maraba Mubi.

LABARAI MASU NASABA

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

Ya ce nan take rundunar ta tattara jami’anta da ke da alaka da Hukumar Leken Asiri ta Jihar (SIB) suka gudanar da aikin, an kuma yi nasara.

A cewarsa, an samu nasarar kwato makudan kudi har miliyan hudu da da dubu saba’in da tara daga cikin Naira miliyan biyar, da aka biya a matsayin kudin fansa.

Ya ce wadanda ake zargin sun hada baki ne suka tafi da wanda suka sace inda suka tsare shi har na tsawon kwanaki biyu har sai an biya su kudin fansa miliyan biyar kamar yadda suka nema kafin a sako wanda abun ya shafa.

A cewarsa, kwamishinan ‘yansandan, SK Akande, yayin da yake yabawa jami’an bisa yadda suka katse hanyoyin sadarwa ta hanyar nuna kwarewa, ya umarci jami’an da su ci gaba da gudanar da irin wannan aikin, a matsayin dabarun binciken laifuka da masu aikata laifuka a cikin jihar da kewaye.

“CP ya yi kira ga jama’a da su sanar da ‘yansanda a ko da yaushe game da inda masu laifi suke da maboyarsu, musamman ma wadanda ke da ake da kokwanto a kan su,” in ji shi.

MASU ALAKA

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano
Labarai

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi
Labarai

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara
Rahotonni

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Next Post
Mbappe Ne Ya Fi Kowanne Dan Wasa Daraja

Mbappe Ne Ya Fi Kowanne Dan Wasa Daraja

LABARAI MASU NASABA

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.