ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansandan Sun Cafke Mutane 5 Kan Zargin Yin Garkuwa Da Mutane, Sun Kwato Miliyan 4 

by Sadiq
4 years ago
'Yansanda

Rundunar ‘yansandan Jihar Adamawa, ta ce jami’anta sun kama wasu mutane biyar da ake zargin masu garkuwa da mutane ne. 

Ta kuma kara da cewa jami’an sun kwato kudi Naira miliyan 4,079,000 daga hannun wadanda ake zargin.

  • ‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2, Sun Kwato Makamai 
  • Gwamnatin Kogi Ta Bai Wa Dangote Sa’o’i 48 Ya Kulle kamfanin Simintinsa Da Ke Obajana

Hakan na kunshe ne a wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yansandan jihar Adamawa, SP Suleiman Yahaya Nguroje, ya fitar ranar Juma’a.

ADVERTISEMENT

A cewar sanarwar, jami’an rundunar, a ranar 9/10/2022, sun katse wata hanyar sadarwa da ke da alaka da kungiyoyin ta’addanci guda biyar a kananan hukumomin Mubi ta Arewa da Kudu.

Rundunar ta ce jami’an sun samu rahoton yin garkuwa da wani matashi mai suna Mustapha Aliyu Fadil dan shekara 8 a garin Mubi tare da kai shi otal din Barassa da ke Maraba Mubi.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Ya ce nan take rundunar ta tattara jami’anta da ke da alaka da Hukumar Leken Asiri ta Jihar (SIB) suka gudanar da aikin, an kuma yi nasara.

A cewarsa, an samu nasarar kwato makudan kudi har miliyan hudu da da dubu saba’in da tara daga cikin Naira miliyan biyar, da aka biya a matsayin kudin fansa.

Ya ce wadanda ake zargin sun hada baki ne suka tafi da wanda suka sace inda suka tsare shi har na tsawon kwanaki biyu har sai an biya su kudin fansa miliyan biyar kamar yadda suka nema kafin a sako wanda abun ya shafa.

A cewarsa, kwamishinan ‘yansandan, SK Akande, yayin da yake yabawa jami’an bisa yadda suka katse hanyoyin sadarwa ta hanyar nuna kwarewa, ya umarci jami’an da su ci gaba da gudanar da irin wannan aikin, a matsayin dabarun binciken laifuka da masu aikata laifuka a cikin jihar da kewaye.

“CP ya yi kira ga jama’a da su sanar da ‘yansanda a ko da yaushe game da inda masu laifi suke da maboyarsu, musamman ma wadanda ke da ake da kokwanto a kan su,” in ji shi.

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
Labarai

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
Next Post
Mbappe Ne Ya Fi Kowanne Dan Wasa Daraja

Mbappe Ne Ya Fi Kowanne Dan Wasa Daraja

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.