A halin yanzu dai shugaba Bola Tinubu yana ganawa da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben 2023, Sanata Rabi’u Musa Kwakwaso.
Idan za a tuna cewa tsohon gwamnan Jihar Kano ya zo na hudu a zaben shugaban kasa da ya gabata.
A cikin kwanaki biyun da suka gabata shugaban ya gana da gwamnonin adawa.
A baya shugaba Tinubu ya gana da Kwankwaso a kasar Faransa, inda wasu majiyoyi suka ce ya yi wa tsohon gwamnan na Kano tayin kujerun minista guda biyu.
Sai dai waccar ganawar tasu ba ta yi wa wasu jiga-jigan jam’iyyar APC dadi ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp