ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Shin Tinubu Zai Iya Kai Bantensa Bisa Yadda Ya Fara?

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Biyo bayan ganawar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi da hafsoshin tsaro a makon da ya gabata bayan hawansa mulki tare da karanta masu karatun-ta-natsu, miliyoyin ‘yan Nijeriya na fatan cewa za a samu gagarumin sauyi kan yanayin rashin tsaro tare dawo da Nijeriya cikin hayyacinta.

Tun bayan da aka rantsar da shi a matsayin zababben shugaban kasar Nijeriya na 16, Tinubu ya dai gaji tsohon Shugaban kasa Muhammadu Buhari. Bayan rantsar da shi, wata tambaya daya ke ci gaba da yawo a zukatan ‘yan Nijeriya da dama shi ne, Shin ko Tinubu zai iya cika alkawarin da ya dauka na magance matsalar rashin tsaro da kasar nan ke fama da shi.

  • Jami’an Amurka Ba Za Su Iya Dakatar Da Matakan Sulhu Na Kasashen Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba
  • Tinubu Zai Gana Da Zababbun Sanatoci A Gobe Alhamis

Bisa kididdigar kashe-kashen da aka yi a Nijeriya da wata cibiyar bincike ta Amurka ta fitar, ya nuna cewa an kashe akalla mutane 89,920 a Nijeriya sakamakon tashe-tashen hankula a cikin shekaru bakwai na farko na gwamnatin Buhari daga Mayu 2015 zuwa Mayu 2022.

Ita ma wata kungiya da ta sadaukar da kai wajen bin diddigin tashe-tashen hankula a Nijeriya ta fitar da rahotonta na shekarar 2023, wanda ya nuna cewa an kashe mutane 1,230 a kasar a rubu’in farko na shekarar 2023.

Rahoton ya kuma ce jami’an tsaro 79 ne suka mutu a cikin wannan lokaci, yayin da aka yi garkuwa da mutane 658 a fadin kasar.

ko bayan rantsar da Tinubu an ci gaba da kashe mutane tare da yin garkuwa da wasu da dama a cikin Nijeriya.

A daidai lokacin da Shugaba Tinubu ya hau kan karagar mulki, idanun ‘yan Nijeriya sun koma kansa tare da yi masa fatan alkairi na ganin ya magance kalubalen da ke gaban kasar nan, nusamman ma a bangaren tsaro. ‘Yan Nijeriya dai na sha’awar samar da kasa mai cike da tsaro, domin su samu nasarar yin barci da idanuwansu guda biyu ba tare da wata fargaba ba.

Bisa kudurinsa na magance tsaro, Tinubu ya yi ganawarsa ta farko da hafsoshin tsaron kasar nan, inda ya bayyana musu cewa bu sauran bayar da uzuri a bangaren jami’an tsaro.

Ya kuma bayyana musu cewa ba zai yarda da halin da al’ummar kasa ke ci gaba da raguwa ba. A cewar shugaban, a yanayin da yake ciki a halin yanzu, dole ne a hada kan tsaron kasa wajen ceto kasar nan.

Shugaban ya umarci hukumomin tsaro da su fito da wani tsari na magance matsalar rashin tsaro a Nijeriya. Ya ce ba shi da isasshen lokaci dole ne a gudanar da sauye-sauyen da suka dace da wuri-wuri.

Taron wanda shi ne na farko da hafsoshin tsaro, ya kasance karkashin jagorancin babban hafsan tsaro, Janar Lucky Irabor. Sauran wadanda suka halarci taron sun hada da babban hafsan sojin kasa, Laftanar Janar Farouk Yahaya da babban hafsan sojin ruwa, Bice Admiral Awwal Gambo da shugaban hafsan sojan sama, Air Marshal Isiaka Amao da babban sufetan ‘yansanda, Usman Alkali Baba.

Tinubu
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
… A Makon Farkon Mulkin Tinubu, Mutum 78 Sun Mutu Tare Da Garkuwa Da 12

... A Makon Farkon Mulkin Tinubu, Mutum 78 Sun Mutu Tare Da Garkuwa Da 12

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.