ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Shin Tinubu Zai Iya Kai Bantensa Bisa Yadda Ya Fara?

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Biyo bayan ganawar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi da hafsoshin tsaro a makon da ya gabata bayan hawansa mulki tare da karanta masu karatun-ta-natsu, miliyoyin ‘yan Nijeriya na fatan cewa za a samu gagarumin sauyi kan yanayin rashin tsaro tare dawo da Nijeriya cikin hayyacinta.

Tun bayan da aka rantsar da shi a matsayin zababben shugaban kasar Nijeriya na 16, Tinubu ya dai gaji tsohon Shugaban kasa Muhammadu Buhari. Bayan rantsar da shi, wata tambaya daya ke ci gaba da yawo a zukatan ‘yan Nijeriya da dama shi ne, Shin ko Tinubu zai iya cika alkawarin da ya dauka na magance matsalar rashin tsaro da kasar nan ke fama da shi.

  • Jami’an Amurka Ba Za Su Iya Dakatar Da Matakan Sulhu Na Kasashen Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba
  • Tinubu Zai Gana Da Zababbun Sanatoci A Gobe Alhamis

Bisa kididdigar kashe-kashen da aka yi a Nijeriya da wata cibiyar bincike ta Amurka ta fitar, ya nuna cewa an kashe akalla mutane 89,920 a Nijeriya sakamakon tashe-tashen hankula a cikin shekaru bakwai na farko na gwamnatin Buhari daga Mayu 2015 zuwa Mayu 2022.

Ita ma wata kungiya da ta sadaukar da kai wajen bin diddigin tashe-tashen hankula a Nijeriya ta fitar da rahotonta na shekarar 2023, wanda ya nuna cewa an kashe mutane 1,230 a kasar a rubu’in farko na shekarar 2023.

Rahoton ya kuma ce jami’an tsaro 79 ne suka mutu a cikin wannan lokaci, yayin da aka yi garkuwa da mutane 658 a fadin kasar.

ko bayan rantsar da Tinubu an ci gaba da kashe mutane tare da yin garkuwa da wasu da dama a cikin Nijeriya.

A daidai lokacin da Shugaba Tinubu ya hau kan karagar mulki, idanun ‘yan Nijeriya sun koma kansa tare da yi masa fatan alkairi na ganin ya magance kalubalen da ke gaban kasar nan, nusamman ma a bangaren tsaro. ‘Yan Nijeriya dai na sha’awar samar da kasa mai cike da tsaro, domin su samu nasarar yin barci da idanuwansu guda biyu ba tare da wata fargaba ba.

Bisa kudurinsa na magance tsaro, Tinubu ya yi ganawarsa ta farko da hafsoshin tsaron kasar nan, inda ya bayyana musu cewa bu sauran bayar da uzuri a bangaren jami’an tsaro.

Ya kuma bayyana musu cewa ba zai yarda da halin da al’ummar kasa ke ci gaba da raguwa ba. A cewar shugaban, a yanayin da yake ciki a halin yanzu, dole ne a hada kan tsaron kasa wajen ceto kasar nan.

Shugaban ya umarci hukumomin tsaro da su fito da wani tsari na magance matsalar rashin tsaro a Nijeriya. Ya ce ba shi da isasshen lokaci dole ne a gudanar da sauye-sauyen da suka dace da wuri-wuri.

Taron wanda shi ne na farko da hafsoshin tsaro, ya kasance karkashin jagorancin babban hafsan tsaro, Janar Lucky Irabor. Sauran wadanda suka halarci taron sun hada da babban hafsan sojin kasa, Laftanar Janar Farouk Yahaya da babban hafsan sojin ruwa, Bice Admiral Awwal Gambo da shugaban hafsan sojan sama, Air Marshal Isiaka Amao da babban sufetan ‘yansanda, Usman Alkali Baba.

Tinubu
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
… A Makon Farkon Mulkin Tinubu, Mutum 78 Sun Mutu Tare Da Garkuwa Da 12

... A Makon Farkon Mulkin Tinubu, Mutum 78 Sun Mutu Tare Da Garkuwa Da 12

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.