• English
  • Business News
Friday, October 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yar Shekara 11 Mai Baiwar Lissafi A Kano Ta Samu Tallafin Karatu Na Bankin Duniya

by Sulaiman
3 years ago
Bankin Duniya

Saratu Garba, yarinya ‘yar shekara 11 da ba ta zuwa makaranta, ta samu tallafin karatu daga kungiyar ‘Adolescent Girls Initiative for Learning and Empowerment (AGILE), acikin wani shiri da bankin duniya ke tallafawa.

Ƙwararriyar yarinyar ta samu baiwa ne a bangaren Ilimin lissafi, an ya yada bidiyon Saratu kwanan nan a shafukan sada zumunta, anga yadda take wa lissafi watsa-watsa wanda hakan ya jawo hankulan mutane da yawa suka nuna kauna a gareta Sabida basirarta.

  • Matashiya Ta Rataye Kanta Saboda Auren Dole A Kano

A ranar Laraba a Kano, Aliyu Yusuf, jami’in sadarwa na shirin AGILE, ya ce ofishin aikinsu na kasa ya umurci ofishinsu na Kano da ya nemo yarinyar sannan su dauki nauyin Karatunta.

Saratu Garba ta fito ne daga kauyen gwadahi dake masarautar Gaya a jihar Kano.

“A ziyarar da tawagar AGILE ta kai Majalisar Masarautar Gaya, sai aka gayyaci yarinyar da iyayenta zuwa fadar sarkin.

LABARAI MASU NASABA

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

“Wakilan ma’aikatar ilimi ta jihar Kano da tawagar AGILE sun yi wa mai martaba sarki, Alhaji Ali Ibrahim-Abdulkadir bayanin aniyar aikin sauke nauyin karatun yarinyar,” inji shi.

Nan take, Wakilin ma’aikatar Ilimi, Haruna Muhammad-Panidau, ya mika kayan makaranta da jaka da sauran kayan karatu ga yarinyar mai hazaka.

Mai Tsare-tsare na ayyukan shirin AGILE a Kano, Ado Tafida-Zango, shi ma ya mika wa yarinyar Naira 20,000 domin tallafa wa karatun ta.

Saratu ta shaida wa wakilin Kamfanin Dillancin Labarai na NAN, wanda ya ziyarci garinsu, kauyen Gwadahi a Gaya, Saratu ta shaida cewa ta fita makaranta ne a aji hudu na firamare ta koma tallace-tallace.

“Na kware a ilimin lissafi, ko kari, ragi, rarrabawa ko ninkawa. Zan iya lissafin lambobi a cikin miliyoyi a kwakwalwata, ba tare da na rubuta ba ko amfani da kalkuleta.

“Na bar makaranta ne saboda cin zarafin da ‘yan ajinmu ke min, sun kasance suna kirana da sunayen da ba na kauna.

“Ba zan koma waccan makarantar ba. Zan yi farin cikin ci gaba da karatu a wata makaranta, nesa da su,” in ji ta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

September 25, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
Al'ajabi

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
Next Post
Munazzamatu Fityanul Islam Reshen Abuja Ta Nesanta Kanta Da Wata Kungiya Mai Irin Sunanta

Munazzamatu Fityanul Islam Reshen Abuja Ta Nesanta Kanta Da Wata Kungiya Mai Irin Sunanta

LABARAI MASU NASABA

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

October 23, 2025
Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

October 23, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno

October 23, 2025
Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

October 23, 2025
Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

October 23, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kasar Sin Ta Karyata Rahoto Na Zuki-ta-malle Da Wata Cibiyar Binciken Amurka Ta Fitar Game Da Hadin Gwiwar Sin Da Yammacin Afirka

October 23, 2025
An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

October 23, 2025
Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 23, 2025
Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

October 23, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.