ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yar Shekara 11 Mai Baiwar Lissafi A Kano Ta Samu Tallafin Karatu Na Bankin Duniya

by Sulaiman
4 years ago
Bankin Duniya

Saratu Garba, yarinya ‘yar shekara 11 da ba ta zuwa makaranta, ta samu tallafin karatu daga kungiyar ‘Adolescent Girls Initiative for Learning and Empowerment (AGILE), acikin wani shiri da bankin duniya ke tallafawa.

Ƙwararriyar yarinyar ta samu baiwa ne a bangaren Ilimin lissafi, an ya yada bidiyon Saratu kwanan nan a shafukan sada zumunta, anga yadda take wa lissafi watsa-watsa wanda hakan ya jawo hankulan mutane da yawa suka nuna kauna a gareta Sabida basirarta.

  • Matashiya Ta Rataye Kanta Saboda Auren Dole A Kano

A ranar Laraba a Kano, Aliyu Yusuf, jami’in sadarwa na shirin AGILE, ya ce ofishin aikinsu na kasa ya umurci ofishinsu na Kano da ya nemo yarinyar sannan su dauki nauyin Karatunta.

ADVERTISEMENT

Saratu Garba ta fito ne daga kauyen gwadahi dake masarautar Gaya a jihar Kano.

“A ziyarar da tawagar AGILE ta kai Majalisar Masarautar Gaya, sai aka gayyaci yarinyar da iyayenta zuwa fadar sarkin.

LABARAI MASU NASABA

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas

Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar

“Wakilan ma’aikatar ilimi ta jihar Kano da tawagar AGILE sun yi wa mai martaba sarki, Alhaji Ali Ibrahim-Abdulkadir bayanin aniyar aikin sauke nauyin karatun yarinyar,” inji shi.

Nan take, Wakilin ma’aikatar Ilimi, Haruna Muhammad-Panidau, ya mika kayan makaranta da jaka da sauran kayan karatu ga yarinyar mai hazaka.

Mai Tsare-tsare na ayyukan shirin AGILE a Kano, Ado Tafida-Zango, shi ma ya mika wa yarinyar Naira 20,000 domin tallafa wa karatun ta.

Saratu ta shaida wa wakilin Kamfanin Dillancin Labarai na NAN, wanda ya ziyarci garinsu, kauyen Gwadahi a Gaya, Saratu ta shaida cewa ta fita makaranta ne a aji hudu na firamare ta koma tallace-tallace.

“Na kware a ilimin lissafi, ko kari, ragi, rarrabawa ko ninkawa. Zan iya lissafin lambobi a cikin miliyoyi a kwakwalwata, ba tare da na rubuta ba ko amfani da kalkuleta.

“Na bar makaranta ne saboda cin zarafin da ‘yan ajinmu ke min, sun kasance suna kirana da sunayen da ba na kauna.

“Ba zan koma waccan makarantar ba. Zan yi farin cikin ci gaba da karatu a wata makaranta, nesa da su,” in ji ta.

Bankin Duniya
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

MASU ALAKA

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas
Al'ajabi

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas

April 21, 2026
Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar
Al'ajabi

Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar

March 8, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Al'ajabi

Ɓata-gari Sun Kashe Matar Aure Da ’Ya’yanta 3 A Kano

January 21, 2026
Next Post
Munazzamatu Fityanul Islam Reshen Abuja Ta Nesanta Kanta Da Wata Kungiya Mai Irin Sunanta

Munazzamatu Fityanul Islam Reshen Abuja Ta Nesanta Kanta Da Wata Kungiya Mai Irin Sunanta

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.