• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yara 2,300 Da Mata 145 Ke Mutuwa Kul-lum A Nijeriya — NPHCDA

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
1 year ago
NPHCDA

Babban daraktan hukumar kula da lafiya a matakin farko ta kasa (NPHCDA), Dakta Muyi Aina, ya ce, har yanzu mata da dama na rasa rayukansu a Nijeriya sakamakon juna biyu da kuma wurin haihuwa, sannan kuma jarirai da dama ba su samun zarafin kai wa shekaru biyar a duniya sakamakon cuttukan da aka kasa shawo kansu.

 

Aina ya shaida hakan ne a ranar Litinin a Abuja a wajen taron wayar da kai kan rigakafi da batutuwan kula da lafiyar mata da yara wanda gidauniyar Sultan ta fadi tashin wanzar da zaman lafiya (SFPD) da hadin gwiwar NPHCDA suka shirya wa shugabannin addini daga yankin arewacin Nijeriya.

  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Manoma 6 Da Aka Sace A Katsina
  • EFCC Ta Kama Tsohon Gwamnan Taraba Ishaku Kan Zargin Badaƙalar 27bn

Shugaba NPHCDA ya kuma kara da cewa Nijeriya ta samu kesa-kesai 70 na kara-min cutar foliyo Type 2 daga kananan hukumomi 46 a jihohin arewacin Nijeriya 14, inda ya ce an samu wannan ne sakamakon rashin yin rigakafi a kai a kai, yayin da wasu kuma ke kin amsar rigakafin foliyo a lokacin da ake gangamin wayar musu da kai.

“A kowace rana, Nijeriya tana rasa sama da yara ‘yan kasa da shekara 5 guda 2,300 da kuma rasa iyaye mata 145 masu dauke da juna biyu a wajen haihuwa. Dukkanin wadannan mace-macen na faruwa ne a yankin arewaci.

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

“Dole ne a canza wannan matsalar. Dole mu tabbatar kowace mace na sun zuwa awo da kuma kulawar da suka dace, kowace mace mai juna biyu ta haihu a han-nun kwararrun unguwar zoma, kuma kowani yaro ya samu damar kammala am-sar rigakafin kamar yadda yake kunshe cikin tsarin kasa, kuma a tabbatar sun samu rigakafi a kowani lokaci a gidajensu. In muka hada hannu za mu cimma na-sarar zuwa matakin da babu wani yaro da za a bar shi ba tare da ya samu rigakafi ba.”

Aina ya bukaci shugabannin addini da su kara jan damara da himma domin ganin an samu inganta kiwon lafiyan jama’a. Ya ce, akwai bukatar a cire dabi’ar wariya wajen bayar da kiwon lafiya ga mutane tare da tabbatar da kowa na samun ku-lawar kiwon lafiya yadda ya dace.

Daga bisani ya jinjina wa Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III, da babban Rabaran, Daniel Okoh bisa gayyato shugabannin addinai da sarakuna da suka yi domin samun wannan horon na musamman kan yadda za a kara wayar da kan jama’a game da muhimmancin rigakafi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba
Manyan Labarai

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
Manyan Labarai

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Next Post
An Fara Tantance Mutane 7,000 da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Limanti

An Fara Tantance Mutane 7,000 da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Limanti

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su

November 2, 2025
Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.