• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yarjejeniyar Da Aka Cimma Tsakanin Gwamnati Da NLC

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
NLC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A halin da ake ciki dai Ƙungiyar ƙwadago ta janye shirin shiga yajin aikin da za ta Jagoranta da za a fara a yau Talata.

An cimma wannan ci gaban ne sakamakon wata yarjejeniya da aka cimma tsakanin gwamnatin tarayya da ƙungiyoyin ƙwadago, wanda NLC ke jagoranta a wani zama da ya gudana a jiya Litinin a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

  • DA DUMI-DUMI: Kotu Ta Tsige Gwamnan Nasarawa Na APC Ta Ayyana Umbugadu Na PDP
  • Kotun Zaben Kano: DSS Ta Cafke Matar Da Ta Yi Wa Shettima, Gawuna Da Alkalin Kotun Barazana

Wasu daga cikin muhimman abubuwan da aka cimma a wannan yarjejeniya, sun haɗa da alƙawarin da gwamnatin tarayya ta yi na ƙarin N35,000 ga duk ma’aikata har na tsawon watanni shida daga watan Satumba.

Haka kuma, a cikin yarjejeniyar, akwai, “kafa wani kwamiti mai ƙarfi cikin wata ɗaya, wanda zai duba batun ƙarin albashi ga ma’aikatan ƙasar nan.

“Janye harajin da aka sanya a harkar man gas (Diesel) na tsawon watanni shida daga watan Oktobar 2023.

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

NLC
Wani bangare na shugabannin kungiyoyin kwadago a taron a fadar gwamnati0

“Sanya Naira biliyan 100 don sayo manyan motocin bas-bas masu amfani da man gas na girki don sauƙaƙa wa jama’a hanyar zirga-zirga a duk faɗin ƙasar nan, wanda ake sa ran za a yi a watan Nuwambar nan.

Haka kuma an cimma yarjejeniyar ɗauke haraji ga wasu kamfanoni da ɗaiɗaikun jama’a don sauƙaƙa masu wajen hada-hadar yau da kullum.

Haka kuma an cimma yarjejeniyar sasantawa a ƙungiyar direbobi ta ƙasa ta NURTW, tare da sanya baki a batun soke ƙungiyar masu motocin hN25,000 a duk wata daga watan Oktobar nan ga ‘yan Nijeriya mutum Miliyan15, wanda ya haɗa da tsofaffin ma’aikata masu karɓar fansho.

Akwai kuma ƙara faɗaɗa shirin nan na rabon taki ga manoma a duk faɗin ƙasar.

An kumma cimma matsayar cewa su ma jihohi da Ƙananan Hukumomi, za a ƙarfafa masu gwiwa domin aiwatar da wannan ƙarin albashi ga ma’aikatan su.

“Samar da kuɗaɗe ga matsaƙaita da ƙananan masana’antu, sannan za a mayar da hankali wajen ƙirƙiro da ayyuka ga matasa.

Za kuma a fito da shirin zagaya matatun man fetur ɗin ƙasar nan don tantance irin gyaran da su ke buƙata.

Gwamnatin taraya za ta yi amfani da takardun da kotu ta sahhale ne wajen saka hannu akan wannan yarjejeniyar fahimtar juna cikin mako daya.

Ita dai wannan yarjejeniya ta samu sanya hannun shugaban NLC na ƙas, Joe Ajaero, Sakataren NLC, Emmanuel Ugboaja, shugaba da Sakatare na TUC, Festus Osifo da Nuhu A.

A ɓangaren gwamnatin tarayya, akwai Ministan Ƙwadago, Simon Lalong da Ƙaramin Ministan sa, Nkeiruka Onyejeocha da kuma Ministan yaɗa labarai, Mohammed Idris.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Cire Tallafin feturGwamnatin TarayyaJanye Yajin AikiNlcTUC
ShareTweetSendShare
Previous Post

A Yau Za A Fayyace Gaskiyar Bayanan Takardun Makarantar Tinubu A Turai

Next Post

Cire Tallafin Fetur: Gwamnatin Kaduna Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Abinci

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

3 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

4 hours ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

5 hours ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

7 hours ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

8 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

9 hours ago
Next Post
Gwamnatin Kaduna

Cire Tallafin Fetur: Gwamnatin Kaduna Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Abinci

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.