ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yarjejeniyar Da Aka Cimma Tsakanin Gwamnati Da NLC

by Sulaiman
3 years ago
NLC

A halin da ake ciki dai Ƙungiyar ƙwadago ta janye shirin shiga yajin aikin da za ta Jagoranta da za a fara a yau Talata.

An cimma wannan ci gaban ne sakamakon wata yarjejeniya da aka cimma tsakanin gwamnatin tarayya da ƙungiyoyin ƙwadago, wanda NLC ke jagoranta a wani zama da ya gudana a jiya Litinin a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

  • DA DUMI-DUMI: Kotu Ta Tsige Gwamnan Nasarawa Na APC Ta Ayyana Umbugadu Na PDP
  • Kotun Zaben Kano: DSS Ta Cafke Matar Da Ta Yi Wa Shettima, Gawuna Da Alkalin Kotun Barazana

Wasu daga cikin muhimman abubuwan da aka cimma a wannan yarjejeniya, sun haɗa da alƙawarin da gwamnatin tarayya ta yi na ƙarin N35,000 ga duk ma’aikata har na tsawon watanni shida daga watan Satumba.

ADVERTISEMENT

Haka kuma, a cikin yarjejeniyar, akwai, “kafa wani kwamiti mai ƙarfi cikin wata ɗaya, wanda zai duba batun ƙarin albashi ga ma’aikatan ƙasar nan.

“Janye harajin da aka sanya a harkar man gas (Diesel) na tsawon watanni shida daga watan Oktobar 2023.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

NLC
Wani bangare na shugabannin kungiyoyin kwadago a taron a fadar gwamnati0

“Sanya Naira biliyan 100 don sayo manyan motocin bas-bas masu amfani da man gas na girki don sauƙaƙa wa jama’a hanyar zirga-zirga a duk faɗin ƙasar nan, wanda ake sa ran za a yi a watan Nuwambar nan.

Haka kuma an cimma yarjejeniyar ɗauke haraji ga wasu kamfanoni da ɗaiɗaikun jama’a don sauƙaƙa masu wajen hada-hadar yau da kullum.

Haka kuma an cimma yarjejeniyar sasantawa a ƙungiyar direbobi ta ƙasa ta NURTW, tare da sanya baki a batun soke ƙungiyar masu motocin hN25,000 a duk wata daga watan Oktobar nan ga ‘yan Nijeriya mutum Miliyan15, wanda ya haɗa da tsofaffin ma’aikata masu karɓar fansho.

Akwai kuma ƙara faɗaɗa shirin nan na rabon taki ga manoma a duk faɗin ƙasar.

An kumma cimma matsayar cewa su ma jihohi da Ƙananan Hukumomi, za a ƙarfafa masu gwiwa domin aiwatar da wannan ƙarin albashi ga ma’aikatan su.

“Samar da kuɗaɗe ga matsaƙaita da ƙananan masana’antu, sannan za a mayar da hankali wajen ƙirƙiro da ayyuka ga matasa.

Za kuma a fito da shirin zagaya matatun man fetur ɗin ƙasar nan don tantance irin gyaran da su ke buƙata.

Gwamnatin taraya za ta yi amfani da takardun da kotu ta sahhale ne wajen saka hannu akan wannan yarjejeniyar fahimtar juna cikin mako daya.

Ita dai wannan yarjejeniya ta samu sanya hannun shugaban NLC na ƙas, Joe Ajaero, Sakataren NLC, Emmanuel Ugboaja, shugaba da Sakatare na TUC, Festus Osifo da Nuhu A.

A ɓangaren gwamnatin tarayya, akwai Ministan Ƙwadago, Simon Lalong da Ƙaramin Ministan sa, Nkeiruka Onyejeocha da kuma Ministan yaɗa labarai, Mohammed Idris.

NLC
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara
  • Sulaiman
    Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

MASU ALAKA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
Manyan Labarai

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
Next Post
Gwamnatin Kaduna

Cire Tallafin Fetur: Gwamnatin Kaduna Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Abinci

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.