• English
  • Business News
Monday, May 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yau Kotun Tarayya Za Ta Yanke Hukuncin Masarautar Kano

by Abubakar Sulaiman
11 months ago
in Masarautu, Manyan Labarai
0
Yau Kotun Tarayya Za Ta Yanke Hukuncin Masarautar Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ana zaman dar-dar a Kano a daidai lokacin da babbar kotun tarayya a ƙarƙashin Mai shari’a Muhammad Liman ke shirin yanke hukunci kan soke dokar masarautar Kano. Kotun dai ta tabbatar da hurumin ta a kan ƙarar da ta shafi hakkin dan Adam da Aminu Babba DanAgundi, Sarkin Dawaki Babba ya shigar yana kalubalanci dokar da majalisar dokokin jihar ta yi wa Masarautar inda ya ce hakan tauye masa hakkinsa. Waɗanda suka amsa sun hada da gwamnatin jihar Kano, da majalisar dokokin jihar, da hukumomin tsaro daban-daban.

Kotun zata yanke hukuncin ne a dai dai lokacin da ake ci gaba da tabka rigingimun siyasa kan masarautar. Gwamna Abba Yusuf ya mayar da Muhammadu Sanusi II a matsayin Sarkin Kano bayan ya gyara dokar Masarautar da ta soke masarautun jihar biyar. Wannan matakin dai ya tsige Aminu Ado Bayero, wanda tun daga lokacin ya ƙalubalanci gyaran.

Sarakunan biyu dai na samun goyon bayan ɓangarorin siyasa masu hamayya da juna: Aminu Ado APC ke goyon baya, da kuma Sanusi Lamido da NNPP ke marawa.

Aminu Ado wanda a yanzu jami’an tsaro ke ba shi kariya, yana zaune ne a kusa da gidan gwamnati, yayin da magoya bayan Gwamna Yusuf suka mamaye fadar Sarkin domin nuna goyon bayansu ga Sanusi Lamido II.

Rikicin shari’a da dama dai na faruwa a kan masarautar, ciki har da hukuncin wata babbar kotun tarayya da ta yanke biyan Aminu Ado diyyar Naira miliyan 10 bisa zargin daurin gidan da aka yi masa.

Labarai Masu Nasaba

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci

Yayin da kotu ke yanke hukunci kan makomar sabuwar dokar masarautar, babban lauyan gwamnatin Kano, Haruna Isah Dederi ya zargi wasu bangarori da yunƙurin hukunta jihar bisa rashin adalci. Ya jaddada aniyar gwamnatin jihar na daukaka kara kan hukuncin da kotun tarayya ta yanke na diyyar, yana mai cewa ba a tauye hakkin Aminu Ado ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Alh. Aminu Ado BayeroBayerokanoKotuSunusi Lamido
ShareTweetSendShare
Previous Post

Alhajin Jihar Jigawa Ya Mayar Da Makudan Kudaden Da Ya Tsinta Ga Mai Shi A Makka

Next Post

Dalilin Da Yasa Muke Kwace Kaddarorin Manyan Dillalan Kwaya – Buba Marwa

Related

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar
Manyan Labarai

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

14 hours ago
Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci

2 days ago
Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya
Manyan Labarai

Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya

2 days ago
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
Manyan Labarai

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

3 days ago
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai
Manyan Labarai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

3 days ago
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

3 days ago
Next Post
Dalilin Da Yasa Muke Kwace Kaddarorin Manyan Dillalan Kwaya – Buba Marwa

Dalilin Da Yasa Muke Kwace Kaddarorin Manyan Dillalan Kwaya - Buba Marwa

LABARAI MASU NASABA

A Koyi Darasi Daga Tarihi

A Koyi Darasi Daga Tarihi

May 11, 2025
Kada A Bata Ran Mahaifiya

Kada A Bata Ran Mahaifiya

May 11, 2025
Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato

Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato

May 11, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Akasarin Jama’a Da Cudanyar Cinikayya Tare Da Sin Fiye Da Amurka

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Akasarin Jama’a Da Cudanyar Cinikayya Tare Da Sin Fiye Da Amurka

May 11, 2025
Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

May 11, 2025
Wang Yi: Ziyarar Shugaba Xi A Rasha Ta Kara Yaukaka Kawance Da Daidaito Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Wang Yi: Ziyarar Shugaba Xi A Rasha Ta Kara Yaukaka Kawance Da Daidaito Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

May 11, 2025
Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Bude Taron Ministoci Na Dandalin Sin Da CELAC Karo Na 4

Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Bude Taron Ministoci Na Dandalin Sin Da CELAC Karo Na 4

May 11, 2025
2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

INEC Na Samun Matsin Lamba Don Kar Ta Yi Wa TNN Rajista — Kakakinta

May 11, 2025
Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa

Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa

May 11, 2025
Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

May 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.