• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yawaitar Ambaliyar Ruwa: Ina Mafita?

by Rabi'at Sidi Bala
1 year ago
Ruwa

Shafin taskira shafi ne da ya saba zakulo muku batutuwa daban-daban wadanda suka shafi al’umma.

Tsokacinmu na yau zai yi duba ne game da yanayi da halin da muke tsintar kammu a ciki duk shekara na samun ambaliyar ruwa a wasu garuruwa a Nijeriya.

  • CBN Ya Kaddamar Da Sabbin Ka’idoji Ga Masu Harkar POS
  • Xi Ya Jaddada Ba Da Cikakkiyar Dama Ga Fa’idar Siyasa Ta CPPCC

Kamar yadda wakiliyarmu BILKISU TIJJANI KASSIM ta tattaro mana, akwai wasu mutane da ke ganin hanyar da za a bi wajen magance yawan ambaliyar ruwa a wasu garuruwa a Nijeriya sun hada da rashin daukar matakan da ya dace tun farko daga gwamnati, musamman wajen fitar da hanyoyi da tituna da suka shafi hanyoyin ruwa musamman lokacin damina domin kiyayen hakkokin jama’a, wanda wannan ba karamin tasiri bane ga jama’a.

Rabi’atu Abdullah Muhammad

Ruwa

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Wasu Maza Ke Gudun Auren Mata ‘Yan Boko Masu Kwarewa Da Wayewa?

Yadda Wasu Iyaye Ke Hana ‘Ya’yansu Auren Matan Da Suka Girme Su Da Zawarawa

Assalamu alaikum Warahmatullah

Hanyoyi da ya kamata a bi wajen magance ambaliyar ruwa su ne, duk inda aka san hanyar ruwa ce kada a toshe ta, sannan kuma sai fadama wajen mazaunar ruwa nan ma kada a rufe shi idan ya zama dole sai an rufe to kada a rufe gaba daya sai a bar masa hanya ko kuma wajen fadamar a bar wani bangare kada a rufe gaba daya domin rufewa gaba dayan shike sa idan ruwa ya zo bai samu waje ko hanya sai ya shiga mutane. Allah ya sa mu dace, Allah ya bamu damuna mai albarka ya bamu wucewa lafiya.

Abdurrahman Tijjani

Ruwa

Assalamu alaikum

Hanyoyi da ya kamata a bi wajen magance Ambaliyar Ruwa a Nijeriya su ne, gwamnati ta tashi da gaske ta yi aiki domin fa sai an yi aiki na gaskiya shi ne duk inda aka san garuruwan da ruwa ya fiya yawan zuwa to ya kamata a yi musu hanyoyin ruwa manya-manyan kwalbati wanda idan ruwa ya zo zai iya wucewa ba tare da ya yi barnaba. Sannan kuma rufe hanyoyin ruwa da rufe fadamu su ne manyan abunuwan da yake kawo wannan Ambaliyar saboda da zarar ruwa ya zo hanyarsa ya ga babu inda zai wuce zai yi cikin gari ne, haka ma rufe fadama itama tana daya daga cikin babban abin da yake kawo Ambaliyar ruwa saboda idan ruwa ya zo wajensa ya tad da an rufe to fa zai yi kokarin zama a wajensa ne an ce shi ruwa ba ya manta wajensa ko ba jima ko ba dade sai ya dawo wajansa, to saboda haka rufe fadama gaskiya shima babbar barazana ce ga Ambaliyar ruwa a inda yake. Allah ya sa mudace

Ibrahim Musa Bala

Yadda gwamnati za ta bollowa ambaliyar da ta faru a garuruwa da dama a Nijeriya.

Ya kamata gwamnati ta gina hanyar wucewar ruwa yadda ruwan zai wuce ba tare da hawa kan hanya ba, sannan ta yi kokari karin ajiye abin zubar da shara saboda a daina zubawa ta ko ina don shi ma yana toshe hanyar wucewar ruwa. Sannan mutane ya kamata su bar gina gida a fadama don ruwa ba ya manta hanyarsa dole komai tsawon shekarun da ya dauka ba ya manta hanyar wucewarsa. Kuma Allah ya kara tsare mu baki daya kuma Allah ya kawo wa wadanda abin ya shafe su sauki

Alkazim Garba

Ruwa

Hanyar da gwamnati za ta iya bollowa da magance yawan Ambaliyar ruwa dake faruwa a garuruwa a Nijeriya su ne, da farko hanyar wucewar ruwa ya kamata ya zama a wadacce saboda wani lokacin idan an yi hanyar wucewar ruwa baya da zurfi shi ne idan an yi ruwan sama sai ya yi saurin hawa kan hanyar wuce wa hakan kuma sai ya haifar da ambaliya saboda haka a yi gini mai zurfi. Sannan gurin zubar da bola ya zama akwai tsafta saboda shi ma ya kan jawo ambaliya yayin da bola ta sauka kan hanya ta kan toshe hanyar wucewar ruwa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Me Ya Sa Wasu Maza Ke Gudun Auren Mata ‘Yan Boko Masu Kwarewa Da Wayewa?
Taskira

Me Ya Sa Wasu Maza Ke Gudun Auren Mata ‘Yan Boko Masu Kwarewa Da Wayewa?

August 31, 2025
Yadda Wasu Iyaye Ke Hana ‘Ya’yansu Auren Matan Da Suka Girme Su Da Zawarawa
Taskira

Yadda Wasu Iyaye Ke Hana ‘Ya’yansu Auren Matan Da Suka Girme Su Da Zawarawa

August 17, 2025
Ruwa
Taskira

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
Next Post
Jarumai A Masana’antar Kannywood Sun Jajanta Wa Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Maiduguri

Jarumai A Masana'antar Kannywood Sun Jajanta Wa Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Maiduguri

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

November 5, 2025
Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025
CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

November 5, 2025
Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.