• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yawaitar Ambaliyar Ruwa: Ina Mafita?

by Rabi'at Sidi Bala
1 year ago
Ruwa

Shafin taskira shafi ne da ya saba zakulo muku batutuwa daban-daban wadanda suka shafi al’umma.

Tsokacinmu na yau zai yi duba ne game da yanayi da halin da muke tsintar kammu a ciki duk shekara na samun ambaliyar ruwa a wasu garuruwa a Nijeriya.

  • CBN Ya Kaddamar Da Sabbin Ka’idoji Ga Masu Harkar POS
  • Xi Ya Jaddada Ba Da Cikakkiyar Dama Ga Fa’idar Siyasa Ta CPPCC

Kamar yadda wakiliyarmu BILKISU TIJJANI KASSIM ta tattaro mana, akwai wasu mutane da ke ganin hanyar da za a bi wajen magance yawan ambaliyar ruwa a wasu garuruwa a Nijeriya sun hada da rashin daukar matakan da ya dace tun farko daga gwamnati, musamman wajen fitar da hanyoyi da tituna da suka shafi hanyoyin ruwa musamman lokacin damina domin kiyayen hakkokin jama’a, wanda wannan ba karamin tasiri bane ga jama’a.

Rabi’atu Abdullah Muhammad

Ruwa

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Wasu Maza Ke Gudun Auren Mata ‘Yan Boko Masu Kwarewa Da Wayewa?

Yadda Wasu Iyaye Ke Hana ‘Ya’yansu Auren Matan Da Suka Girme Su Da Zawarawa

Assalamu alaikum Warahmatullah

Hanyoyi da ya kamata a bi wajen magance ambaliyar ruwa su ne, duk inda aka san hanyar ruwa ce kada a toshe ta, sannan kuma sai fadama wajen mazaunar ruwa nan ma kada a rufe shi idan ya zama dole sai an rufe to kada a rufe gaba daya sai a bar masa hanya ko kuma wajen fadamar a bar wani bangare kada a rufe gaba daya domin rufewa gaba dayan shike sa idan ruwa ya zo bai samu waje ko hanya sai ya shiga mutane. Allah ya sa mu dace, Allah ya bamu damuna mai albarka ya bamu wucewa lafiya.

Abdurrahman Tijjani

Ruwa

Assalamu alaikum

Hanyoyi da ya kamata a bi wajen magance Ambaliyar Ruwa a Nijeriya su ne, gwamnati ta tashi da gaske ta yi aiki domin fa sai an yi aiki na gaskiya shi ne duk inda aka san garuruwan da ruwa ya fiya yawan zuwa to ya kamata a yi musu hanyoyin ruwa manya-manyan kwalbati wanda idan ruwa ya zo zai iya wucewa ba tare da ya yi barnaba. Sannan kuma rufe hanyoyin ruwa da rufe fadamu su ne manyan abunuwan da yake kawo wannan Ambaliyar saboda da zarar ruwa ya zo hanyarsa ya ga babu inda zai wuce zai yi cikin gari ne, haka ma rufe fadama itama tana daya daga cikin babban abin da yake kawo Ambaliyar ruwa saboda idan ruwa ya zo wajensa ya tad da an rufe to fa zai yi kokarin zama a wajensa ne an ce shi ruwa ba ya manta wajensa ko ba jima ko ba dade sai ya dawo wajansa, to saboda haka rufe fadama gaskiya shima babbar barazana ce ga Ambaliyar ruwa a inda yake. Allah ya sa mudace

Ibrahim Musa Bala

Yadda gwamnati za ta bollowa ambaliyar da ta faru a garuruwa da dama a Nijeriya.

Ya kamata gwamnati ta gina hanyar wucewar ruwa yadda ruwan zai wuce ba tare da hawa kan hanya ba, sannan ta yi kokari karin ajiye abin zubar da shara saboda a daina zubawa ta ko ina don shi ma yana toshe hanyar wucewar ruwa. Sannan mutane ya kamata su bar gina gida a fadama don ruwa ba ya manta hanyarsa dole komai tsawon shekarun da ya dauka ba ya manta hanyar wucewarsa. Kuma Allah ya kara tsare mu baki daya kuma Allah ya kawo wa wadanda abin ya shafe su sauki

Alkazim Garba

Ruwa

Hanyar da gwamnati za ta iya bollowa da magance yawan Ambaliyar ruwa dake faruwa a garuruwa a Nijeriya su ne, da farko hanyar wucewar ruwa ya kamata ya zama a wadacce saboda wani lokacin idan an yi hanyar wucewar ruwa baya da zurfi shi ne idan an yi ruwan sama sai ya yi saurin hawa kan hanyar wuce wa hakan kuma sai ya haifar da ambaliya saboda haka a yi gini mai zurfi. Sannan gurin zubar da bola ya zama akwai tsafta saboda shi ma ya kan jawo ambaliya yayin da bola ta sauka kan hanya ta kan toshe hanyar wucewar ruwa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Me Ya Sa Wasu Maza Ke Gudun Auren Mata ‘Yan Boko Masu Kwarewa Da Wayewa?
Taskira

Me Ya Sa Wasu Maza Ke Gudun Auren Mata ‘Yan Boko Masu Kwarewa Da Wayewa?

August 31, 2025
Yadda Wasu Iyaye Ke Hana ‘Ya’yansu Auren Matan Da Suka Girme Su Da Zawarawa
Taskira

Yadda Wasu Iyaye Ke Hana ‘Ya’yansu Auren Matan Da Suka Girme Su Da Zawarawa

August 17, 2025
Ruwa
Taskira

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
Next Post
Jarumai A Masana’antar Kannywood Sun Jajanta Wa Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Maiduguri

Jarumai A Masana'antar Kannywood Sun Jajanta Wa Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Maiduguri

LABARAI MASU NASABA

Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

October 15, 2025
Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

October 15, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

October 15, 2025
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Barazana Ce Ga Tsaro A Yammacin Afirka – Tinubu

October 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako

October 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama Mutum 105, Sun Ƙwato Ƙwayoyi Sama Da 5,000 A Jigawa

October 15, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

October 15, 2025
Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

October 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

October 14, 2025
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.