ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CBN Ya Kaddamar Da Sabbin Ka’idoji Ga Masu Harkar POS

by Bello Hamza
2 years ago
CBN

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sanar da sabbin ka’idoji na sarrafa hada-hadar kasuwancin ‘PoS’ a fadin kasar nan, inda ya ba da umarnin cewa duk wani ciniki na POS zai bi ta ta hanyar cibiyar hadakar hada-hadar bankuna wato NIBSS ko UPSL, wanda wannan zai karya ikon tsohon tsarin da ake a kai na sarrafa mu’amalar kudi.

A cikin wata sanarwa mai kwanan ranar 11 ga watan Satumba, 2024 zuwa ga duk masu ba da sabis na hada hadar kudi zuwa kan PTSA (Payment Terminal Serbice Aggregators), CBN ta umurce su da su fara daidaitawa tare da PTSAs sannan su kuma sanar da CBN a rubuce domin tabbatar da bin wannan doka a cikin kwanaki 30 daga kan kwanan watan wannan takarda.

  • Anya Barcelona Za Ta Iya Kai Bantenta Kuwa A Gasar Zakarun Turai Ta Bana?
  • Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Dala Tiriliyan 7 A Tsarin Kasuwancin Musulunci Na Duniya

Domin cimma manufar bin diddigin hada-hadar kasuwancin kudade a Nijeriya, CBN a watan Agustan 2011, ya ba da lasisin PTSA ga NIBSS.

ADVERTISEMENT

Biyo bayan damuwa game da bayar da damar lura da duk wani sha’anin kudi ta PoS ga cibiya guda ɗaya tal, a ranar 19 ga Afrilu, 2024, ta ba da lasisin PTSA na biyu zuwa ga UPSL (Unified Payment Serbices Limited).Kusan watanni biyar bayan da ta ba da lasisi ga UPSL, CBN ya ba da umarnin cewa masu wannan hulda su “sanya duk wata mu’amalar kudi dake gudana a PoS a wuraren kasuwanci imma a zahiri, ko a kan manhajar PoS na zahiri ko na badini, ta hanyar PSTA da suke da lasisi da CBN.”Sanarwar ta ci gaba da cewa, “ana bukatar PTSAs su aika da mu’amalar PoS zuwa ga kawai ma’aikatan da aka sahhalewar lura da tsarin hada hadar kudi, wanda masu sha’anin kudi suka ayyana kuma CBN ta ba su lasisi. Dole ne dukkan masu sarrafawa wadanda suke da lasisi a hada su da PTSAs, ta yadda za a bai wa masu hulda damar zabar wacce hanya da kuma PTSA za su yi amfani da su.“Duk cibiyar da ke lura da sha’anin kudi (PTSPs) dole ne su tabbatar da cewa an saita na’urorin PoS, manhajarsu da ayyukansu da kuma mu’amalar kudada ta hanyar PTSA, kamar yadda aka bada umurni. Duk PTSPs za su gabatar da bayani a kowanne wata ga CBN, suna mai bayyana adadin ‘yan kasuwa da wakilan da suke gudanar da aiki a karkashin su, tare da ayyukan PTSA da ake amfani da su wajen tafiyar da hada-hadar da ta dace.“Kowacce PTSA ana bukatar ya gabatar da kudaden da aka samu a kowanne wata ga CBN, tare da bayar da cikakkun bayanai game da duk wata hada-hadar da aka sarrafa ta hanyoyin sadarwar su. Ana sa ran gabatar da wannan bayani da aka ambata a sama ga Daraktan lura da sashen kula da tsarin biyan Kudi, kasa da kwanaki bakwai bayan karshen kowanne wata.

CBN
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Tattalin Arziki

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Next Post
Sama Da Kasashe Da Hukumomin Kasa Da Kasa 70 Sun Ba Da Tabbacin Halartar Bikin CIIE Karo Na 7

Sama Da Kasashe Da Hukumomin Kasa Da Kasa 70 Sun Ba Da Tabbacin Halartar Bikin CIIE Karo Na 7

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.