• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yawan Masu Zaman Kashe Wando A Nijeriya Ya Ragu Da Kashi 4.3 – NBS

by Yusuf Shuaibu
9 months ago
in Labarai
0
Yawan Masu Zaman Kashe Wando A Nijeriya Ya Ragu Da Kashi 4.3 – NBS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sabon rahoton hukumar ƙididdiga ta kasa (NBS) ta bayyana cewa adadin marasa aikin yi ya ragu zuwa kashi 4.3 a Nijeriya, wanda ya nuna raguwar kashi 0.1 a cikin kwata na biyu na shekarar 2024, idan aka kwatanta da na shekarar da ta gabata.

Adadin rashin aikin yi na matasa ya kasance kashi 6.5 a cikin kwatan shekarar 2024, yana nuna raguwa daga kashi 8.4 a cikin farkon kwatan 2024.

  • Yadda Matatar Mai Ta Fatakwal Ta Fara Aiki
  • Kasar Sin Za Ta Samar Da Ababen Hawa 100,000 Don Aikin Taksi Da Na Amfanin Kai Nan Da Shekarar 2030

Hukumar NBS ta fitar da rahoton kwata-kwata a ranar Litinin, wanda kuma ya nuna cewa rashin aikin yi a tsakanin maza ya kai kashi 3.4 da 5.1 a tsakanin mata.

A wurin zama kuma, yawan marasa aikin yi ya kai kashi 5.2 a birane da kashi 2.8 a yankunan karkara.
Alƙaluman NBS sun nuna cewa a kashi na biyu na shekarar 2024, yawan ‘yan Nijeriya marasa aikin yi ya kai kashi 9.2, ya ragu da kashi 1.4 cikin dari daga kashi 10.6 da aka samu a farkon kwatan 2024.

Rabon mazan da ba su da aikin yi ya kai kashi 7.1, yayin da mata ke fama da rashin aikin yi da kashi 11.2 na kwatan wannan shekara.
A gefe guda kuma, a cikin rubu’in shekarar 2024, adadin ma’aikata a Nijeriya ya kasance kashi 76.1 na yawan mutanen da suka yin aiki, sama da 73.1 a cikin farkon kwatan 2024.

Labarai Masu Nasaba

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

Dangane da jinsi kuma, yawan maza masu aiki yi ya kai kashi 77.2 da 75 na mata a cikin rubu’in shekarar 2024.
A cewar NBS, sabon alƙaluman ya nuna karuwar kashi 2.9 na ma’aikata idan aka kwatanta da kashi 73.2 a cikin farkon kwatan 2024. Duk da haka, kwatankwacin shekara na nuna raguwa kadan daga kashi 77.1 a 2023 Bugu da kari, yawan masu aikin yi a cikin birane ya kasance 73.2 da 80.8 a yankunan karkara a cikin rabin shekarar 2024.

NBS ta bayyana hakan ne a cikin rahoton da ta wallafa a shafinta na yanar gizo, inda ta ce, “Wannan wani karin ci gaba ne idan aka kwatanta da kashi 69.5 da kashi 78.9 a farkon kwatan shekarar 2023.

Adadin shiga aiki a tsakanin yawan shekarun aiki ya ƙaru zuwa 79.5 a cikin kwata na biyu na shekarar 2024 daga kashi 77.3 a farkon kwatan 2024.
Aiki na yau da kullun ya kasance mai girma na kashi 93. ƙididdigar ofishin ta ce kashi 3.7 na yawan mutanen da suka yi aiki suna noma ne a cikin kashi na biyu na shekarar 2024.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Aiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Matatar Mai Ta Fatakwal Ta Fara Aiki

Next Post

An Fitar Da Jigo Da Tambarin Shirye-Shiryen Murnar Bikin Sabuwar Shekarar Sinawa na CMG Na 2025

Related

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato
Labarai

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

27 minutes ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

2 hours ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

5 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

6 hours ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

14 hours ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

18 hours ago
Next Post
An Fitar Da Jigo Da Tambarin Shirye-Shiryen Murnar Bikin Sabuwar Shekarar Sinawa na CMG Na 2025

An Fitar Da Jigo Da Tambarin Shirye-Shiryen Murnar Bikin Sabuwar Shekarar Sinawa na CMG Na 2025

LABARAI MASU NASABA

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

August 22, 2025
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

August 22, 2025
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

August 22, 2025
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

August 22, 2025
Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

August 22, 2025
Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

August 22, 2025
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

August 22, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

August 22, 2025
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.