ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yawan Masu Zaman Kashe Wando A Nijeriya Ya Ragu Da Kashi 4.3 – NBS

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Nijeriya

Sabon rahoton hukumar ƙididdiga ta kasa (NBS) ta bayyana cewa adadin marasa aikin yi ya ragu zuwa kashi 4.3 a Nijeriya, wanda ya nuna raguwar kashi 0.1 a cikin kwata na biyu na shekarar 2024, idan aka kwatanta da na shekarar da ta gabata.

Adadin rashin aikin yi na matasa ya kasance kashi 6.5 a cikin kwatan shekarar 2024, yana nuna raguwa daga kashi 8.4 a cikin farkon kwatan 2024.

  • Yadda Matatar Mai Ta Fatakwal Ta Fara Aiki
  • Kasar Sin Za Ta Samar Da Ababen Hawa 100,000 Don Aikin Taksi Da Na Amfanin Kai Nan Da Shekarar 2030

Hukumar NBS ta fitar da rahoton kwata-kwata a ranar Litinin, wanda kuma ya nuna cewa rashin aikin yi a tsakanin maza ya kai kashi 3.4 da 5.1 a tsakanin mata.

ADVERTISEMENT

A wurin zama kuma, yawan marasa aikin yi ya kai kashi 5.2 a birane da kashi 2.8 a yankunan karkara.
Alƙaluman NBS sun nuna cewa a kashi na biyu na shekarar 2024, yawan ‘yan Nijeriya marasa aikin yi ya kai kashi 9.2, ya ragu da kashi 1.4 cikin dari daga kashi 10.6 da aka samu a farkon kwatan 2024.

Rabon mazan da ba su da aikin yi ya kai kashi 7.1, yayin da mata ke fama da rashin aikin yi da kashi 11.2 na kwatan wannan shekara.
A gefe guda kuma, a cikin rubu’in shekarar 2024, adadin ma’aikata a Nijeriya ya kasance kashi 76.1 na yawan mutanen da suka yin aiki, sama da 73.1 a cikin farkon kwatan 2024.

LABARAI MASU NASABA

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

Dangane da jinsi kuma, yawan maza masu aiki yi ya kai kashi 77.2 da 75 na mata a cikin rubu’in shekarar 2024.
A cewar NBS, sabon alƙaluman ya nuna karuwar kashi 2.9 na ma’aikata idan aka kwatanta da kashi 73.2 a cikin farkon kwatan 2024. Duk da haka, kwatankwacin shekara na nuna raguwa kadan daga kashi 77.1 a 2023 Bugu da kari, yawan masu aikin yi a cikin birane ya kasance 73.2 da 80.8 a yankunan karkara a cikin rabin shekarar 2024.

NBS ta bayyana hakan ne a cikin rahoton da ta wallafa a shafinta na yanar gizo, inda ta ce, “Wannan wani karin ci gaba ne idan aka kwatanta da kashi 69.5 da kashi 78.9 a farkon kwatan shekarar 2023.

Adadin shiga aiki a tsakanin yawan shekarun aiki ya ƙaru zuwa 79.5 a cikin kwata na biyu na shekarar 2024 daga kashi 77.3 a farkon kwatan 2024.
Aiki na yau da kullun ya kasance mai girma na kashi 93. ƙididdigar ofishin ta ce kashi 3.7 na yawan mutanen da suka yi aiki suna noma ne a cikin kashi na biyu na shekarar 2024.

Nijeriya
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

MASU ALAKA

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta
Labarai

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

July 21, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC
Labarai

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

July 21, 2026
Next Post
An Fitar Da Jigo Da Tambarin Shirye-Shiryen Murnar Bikin Sabuwar Shekarar Sinawa na CMG Na 2025

An Fitar Da Jigo Da Tambarin Shirye-Shiryen Murnar Bikin Sabuwar Shekarar Sinawa na CMG Na 2025

LABARAI MASU NASABA

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao

Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao

July 21, 2026
An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026

An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026

July 21, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

July 21, 2026
Li Qiang Ya Taya Andy Burnham Murnar Zama Sabon Firaministan Birtaniya

Li Qiang Ya Taya Andy Burnham Murnar Zama Sabon Firaministan Birtaniya

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida

Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida

July 21, 2026
Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule

Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Bayar Da Tallafin Sama Da Ton 3,000 Na Abinci Ga Sudan Ta Kudu

Kasar Sin Ta Bayar Da Tallafin Sama Da Ton 3,000 Na Abinci Ga Sudan Ta Kudu

July 21, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Harbe Mai Unguwa Har Lahira A Bauchi

July 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.